Matsalar rashin tsaro na ƙara jefa manoma a Arewa Maso Yammacin Nijeriya cikin matsala, inda tsoron hare-haren ‘yan bindiga ke hana wasu zuwa gonakinsu ko yin noma yadda ya kamata.
A wasu sassan Zamfara, Katsina, Sakkwato da Kaduna, manoma na fuskantar barazanar garkuwa, kisa da hare-hare a gonakinsu.
Wasu kuma na tsoron zuwa gonakinsu saboda ‘yan bindiga na iya kai musu hari ko garkuwa da su.
A kan hanyar Zariya zuwa Sakkwato, musamman tsakanin Funtua da Gusau, rashin tsaro ya sa hukumomi suka hana manoma shuka amfanin gona masu tsayi a kusa da hanya.
Ana ganin ‘yan bindiga na amfani da dogayen amfanin gona wajen fakewa da kai wa matafiya da jami’an tsaro hari.
Saboda haka, manoma da ke kusa da manyan hanyoyi sun koma noman gyaɗa, wake, waken soya, shinkafa da dankali, waɗanda ba sa yin tsayi sosai.
Sai dai matsalar ta fi gaban haka, saboda wasu manoma sun ce tsoron ‘yan bindiga yana hana su zuwa gonaki, musamman a wuraren da aka samu yawaitar hare-hare da satar mutane.
Wani manomi a yankin Tsafe na Zamfara ya ce akwai lokutan da yake kasa zuwa gonarsa saboda tsoron kai masa hari.
Ya ce ɗan uwansa ya taɓa shafe kwanaki 11 a hannun ‘yan bindiga bayan an sace shi a gidansu, yayin da wasu manoma da suka je cirar rogo su ma aka sace.
Manoman sun ce rashin tsaro yana su zuwa yin noma, wanda ke shafar abin da suke samu da kuma samar da abinci ga al’umma.
Wasu daga cikinsu sun ce da babu matsalar tsaro, za su noma masara, dawa da gero tare da sauran amfanin gona.
Amma yanzu suna tilasta wa kansu yin noman da za su iya yi saboda fargaba.
Masana na ganin idan ba a magance matsalar tsaro ba, harkar noma a yankin za ta ci gaba da fuskantar koma baya, lamarin da ka iya ƙara tsadar kayan abinci da ƙarancin amfanin gona.














