Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Musa Ayuba Lukuwa ya jagoranci al’ummar Musulmi gudanar da Sallar Idi a masallacinsa da ke Sakkwato.
Malamin ya jagoranci sallar ne da misalin ƙarfe 9 na safe.
- Adadin Mayaƙan ISWAP Da Aka Kashe A Borno Ya Kai 75
- Shettima Ya Ziyarci Waɗanda Harin Bam Ya Shafa A Maiduguri
Malamin ya ce sun gamsu da sanarwar ganin wata da hukumomin Jamhuriyar Nijar suka bayyana wanda a hukumance gwamnatin ƙasar ta tabbatar da ganinsa.
Ya ce “Mun yi sallah ne a bisa ga faɗar Manzon Allah, Annabi Muhammad (S.A.W) wanda ya ce idan an ga wata wato idan Sha’aban ya kai 29 ko 30 a ajiye azumi, haka ma idan Ramadan ya ƙare da adadin kwanaki 29 ko 30 don haka muka yi ɗa’a da bin umarnin Manzon Allah.”
A tsawon shekaru dai Malamin wanda ke da tarin mabiya bai saba yin sallah da sanarwar mai Alfarma Sarkin Musulmi ba tare da miliyoyin al’umma.
Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar a daren jiya ya bayyana sanarwar rashin ganin watan Shawwal tare da bai wa al’ummar Musulmi umarnin su cika azumi 30 da yin sallah a ranar Juma’a.
















