Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle ya bukaci magoya bayansa da su mara wa wa’adi na biyu na Shugaba Bola Ahmad Tinubu da Gwamna Dauda Lawal baya a babban zaben 2027 mai zuwa.
Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da yake jawabi ga dimbin magoya bayansa a dakin taron Garba Nadama da ke sakatariyar J B Yakubu.
Bello Matawalle ya ce wadannan manyan mutane guda biyu sun yi kokari matuka wajen gudanar da ayyukansu a matsayin shugaban kasa da gwamna.
Ya ce su biyun sun cancanci a sake zabarsu wa’adi na biyu don su ci gaba da kyakkyawan aikin da suka fara.
Ya kara da cewa, Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi kokari matuka wajen magance matsalar rashin tsaro da ‘yan ta’adda a Nijeriya musamman a jihar Zamfara.
Ya yaba musu kan tsayuwarsu da goyon bayan da suke bayarwa kuma ya bukace su da su ci gaba da hakan.















Discussion about this post