Kyaftin ɗin tawagar Super Eagles ta Nijeriya Wilfred Ndidi ya yi watsi da maganar rashin jituwa tsakanin Ɓictor Osimhen da Ademola Lookman, yana mai bayyana rashin jituwarsu a filin wasa a daren Litinin, inda Nijeriya ta doke Mozambiƙue a matsayin ƙaramar rigima tsakanin manyan ƴan wasan biyu.
Ndidi ya yi magana kan batun yayin da yake magana da ESPN bayan nasarar 4-0 da Nijeriya ta samu akan Mozambiƙue a gasar AFCON 2025, yana mai bayyana cewa ba wani abu bane mai matsala kawai dai ƴan wasan ne ke neman ƙarin fahimtar juna a yayin taka leda a cikin fili, ɗan wasan tsakiyar ya ƙara da cewa an warware lamarin cikin sauri a cikin tawagar yana mai cewa babu wani tashin hankali da ke tsakanin ƴan wasan a halin yanzu.
“Komai yana lafiya, kuma mun shawo kan lamarin a cikin ɗakin sanya kaya, yanzu komai yana tafiya yadda ya kamata, hakazalika Lookman ya yi watsi da lamarin, yana sake tabbatar da girmamawarsa ga Osimhen da kuma ƙarfin haɗin gwiwa da girmama juna dake cikin tawagar, ban ga Osimhen ba, shi ne mutum na farko a tawagarmu, kowa ya san wannan shi babban ɗan wasan gaba ne, don haka komai ya daidaita” in ji gwarzon ɗan ƙwallon ƙafar Afirika na shekarar 2024.














