Tawagar ƙwallon ƙafa ta Senegal ta tsallake zuwa zagaye na 32 a Gasar Kofin Duniya ta 2026 bayan ta doke Iraki da ci 5-0 a wasanta na uku na rukuni.
Duk da shan kashi a hannun Faransa da Norway a wasanninta biyu na farko, Senegal ta kammala matakin rukuni da maki uku, inda ta tsallaka a matsayin ɗaya daga cikin mafi kyawun ƙasashen da suka zo na uku a rukunoninsu.
A ɗaya ɓangaren, wannan rashin nasara ya tabbatar da ficewar Iraki daga gasar bayan ta kammala a ƙarshen rukuninta ba tare da samun ko maki ɗaya ba. Haka kuma, an zura mata ƙwallaye 11 a wasanni uku, mafi yawa da aka ci wa kowace ƙasa a gasar zuwa yanzu.
Nasarar Senegal ta kuma rage wa Scotland damar tsallakawa zuwa zagaye na gaba, bayan ƙasashen biyu sun kammala da maki uku, amma Senegal ta fi ta yawan ƙwallaye.














