ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisar PDP Sun Yi Allah-wadai Da Zargin Alaƙanta Gwamnan Bauchi Da Ɗaukar Nauyin Ta’addanci

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
5 months ago
Bala Mohammed

’Yan Majalisar Wakilai na Jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi sun bayyana cikakken goyon baya da biyayya ba tare da tangarɗa ba ga Gwamna Bala Muhammad, bisa abin da suka kira “yaɓa masa zargin alaka da ɗaukan nauyin ayyukan ta’addanci”.

 

A cikin wata sanarwa da suka fitar ga manema labarai jiya a Bauchi, ƙungiyar ‘yan majalisan ta ce duk da cewa batun yana gaban kotu a halin yanzu, ya zama dole a tunatar da ‘yan Nijeriya tarihin Gwamna Bala Mohammed na bada fifiko da muhimmanta harkokin tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban Jihar Bauchi a kowane lokaci.

ADVERTISEMENT
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙaƙaba Haraji Kan Ƙasashen Da Ke Kasuwanci Da Iran
  • AFCON 2025: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Karawar Nijeriya Da Morocco

“Yana da muhimmanci mu jaddada ingantaccen tarihi na Gwamna Bala Mohammed a matsayin shugaba da ya dinga sanya kwanciyar al’umma da tsaronsu da ci gaban Jihar Bauchi sama da komai,” In ji sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Sanarwar ta samu sa hannun ’yan Majalisar Wakilai na tarayya bakwai na PDP daga Jihar Bauchi da suka haɗa da Hon. Aliyu Aminu Garu (Mazaɓar Tarayya ta Bauchi), Hon. Mansur Manu Soro (Darazo/Ganjuwa), Hon. Auwalu Gwalabe (Katagum), Hon. Adamu Hashimu Ranga (Ningi/Warji), Hon. Mohammed Dan Abba Shehu (Zaki), Hon. Bappa Aliyu Misau (Misau/Dambam), da Hon. Sani Ibrahim Tanko (Da ke wakiltar Mazaɓar Shira/Giade).

 

A cewar ƙungiyar, Gwamna Bala Mohammed ya yi nasarar rage ayyukan ‘yan fashi da makami a Jihar Bauchi tsawon shekaru shida da suka gabata, duk da wata matsalar tsaro da ke tasowa sakamakon makwabtakar jihar da jihohin da ke fama da matsalar fashi da makami kamar Zamfara da Katsina.

 

“A daidai lokacin da matsalar tsaro ta tilasta wa jama’a yin ƙaura a Arewa maso Yamma da wasu sassan ƙasar nan, Jihar Bauchi ta ci gaba da kasancewa cikin aminci kuma wurin samun mafaka, sakamakon shugabanci mai inganci da hangen nesa da kuma shirin ko ta kwana ga matsalolin tsaro,” In ji su.

 

‘Yan Majalisar sun kuma jaddada cewa duk da kasancewar Jihar Bauchi a yankin Arewa Maso Gabas, ta ci gaba da kasancewa babu tasirin ta’addancin Boko Haram a duk tsawon mulkin Gwamna Bala Mohammed.

 

“Wannan nasara ba ta zo haka nan ba. Ta samo asali ne daga manufofi na gangan, kyakkyawar haɗin gwiwa da hukumomin tsaro, da ƙudurin gwamna na hana ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka samun kafar zama a jihar,” sanarwar ta ƙara da cewa.

 

Ƙungiyar ta bayyana zarge-zargen da ke alaƙanta gwamnan da ɗaukar nauyin ta’addanci a matsayin zargin da hankali ba zai ɗauka ba lura da azamar gwamnan na kyautata harkokin tsaro, kuma zargin ya saɓanin haƙiƙankn abin da mutanen Jihar Bauchi shaidawa na samun ingancin tsaro da kwanciyar hankali a zahirance.

 

“Gwamna da ya dinga hana ‘yan ta’adda samun sarari, ya kare al’umma, kuma ya tabbatar da dorewar zaman lafiya ba za a iya kiran sa mai ɗaukar nauyin ta’addanci ba ta kowace hanya,” In ji su.

 

Baya ga tsaro, ‘yan majalisan su haskaka abin da suka kira manyan nasarori da ba a taɓa ganin irinsu ba a fannonin ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da walwalar jama’a a tsawon shekaru shida na mulkin Gwamna Bala Mohammed.

 

“Waɗannan nasarori sun fi kowace yekuwar siyasa, kuma suna bayyana ƙudurin gwamna na kyakkyawan shugabanci da mayar da hankali kan jin daɗin jama’a,” In ji sanarwar.

 

Ƙungiyar ‘yan majalisun PDP ta Bauchi ta yi kira ga ’yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu tare da yin nazari mai kyau, tana mai roƙon jama’a su mutunta doka da oda tare da barin gaskiya ta bayyana kanta ta hanyoyin da doka ta tanada.

 

“Muna da cikakken tabbacin cewa mutuncin Gwamna Bala Mohammed, tarihinsa na aiki da hidimarsa ga Jihar Bauchi za su tabbata a ƙarshe,” in ji sanarwar a ƙarshe.

PDP
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina
Labarai

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta
Tsaro

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Next Post
Ci Gaban Kirkire-kikiren Kasar Sin: Abin Da Wasu Manyan Jaridun Duniya Suka Fada

Ci Gaban Kirkire-kikiren Kasar Sin: Abin Da Wasu Manyan Jaridun Duniya Suka Fada

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.