ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisar PDP Sun Yi Allah-wadai Da Zargin Alaƙanta Gwamnan Bauchi Da Ɗaukar Nauyin Ta’addanci

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Bala Mohammed

’Yan Majalisar Wakilai na Jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi sun bayyana cikakken goyon baya da biyayya ba tare da tangarɗa ba ga Gwamna Bala Muhammad, bisa abin da suka kira “yaɓa masa zargin alaka da ɗaukan nauyin ayyukan ta’addanci”.

 

A cikin wata sanarwa da suka fitar ga manema labarai jiya a Bauchi, ƙungiyar ‘yan majalisan ta ce duk da cewa batun yana gaban kotu a halin yanzu, ya zama dole a tunatar da ‘yan Nijeriya tarihin Gwamna Bala Mohammed na bada fifiko da muhimmanta harkokin tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban Jihar Bauchi a kowane lokaci.

ADVERTISEMENT
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙaƙaba Haraji Kan Ƙasashen Da Ke Kasuwanci Da Iran
  • AFCON 2025: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Karawar Nijeriya Da Morocco

“Yana da muhimmanci mu jaddada ingantaccen tarihi na Gwamna Bala Mohammed a matsayin shugaba da ya dinga sanya kwanciyar al’umma da tsaronsu da ci gaban Jihar Bauchi sama da komai,” In ji sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Sanarwar ta samu sa hannun ’yan Majalisar Wakilai na tarayya bakwai na PDP daga Jihar Bauchi da suka haɗa da Hon. Aliyu Aminu Garu (Mazaɓar Tarayya ta Bauchi), Hon. Mansur Manu Soro (Darazo/Ganjuwa), Hon. Auwalu Gwalabe (Katagum), Hon. Adamu Hashimu Ranga (Ningi/Warji), Hon. Mohammed Dan Abba Shehu (Zaki), Hon. Bappa Aliyu Misau (Misau/Dambam), da Hon. Sani Ibrahim Tanko (Da ke wakiltar Mazaɓar Shira/Giade).

 

A cewar ƙungiyar, Gwamna Bala Mohammed ya yi nasarar rage ayyukan ‘yan fashi da makami a Jihar Bauchi tsawon shekaru shida da suka gabata, duk da wata matsalar tsaro da ke tasowa sakamakon makwabtakar jihar da jihohin da ke fama da matsalar fashi da makami kamar Zamfara da Katsina.

 

“A daidai lokacin da matsalar tsaro ta tilasta wa jama’a yin ƙaura a Arewa maso Yamma da wasu sassan ƙasar nan, Jihar Bauchi ta ci gaba da kasancewa cikin aminci kuma wurin samun mafaka, sakamakon shugabanci mai inganci da hangen nesa da kuma shirin ko ta kwana ga matsalolin tsaro,” In ji su.

 

‘Yan Majalisar sun kuma jaddada cewa duk da kasancewar Jihar Bauchi a yankin Arewa Maso Gabas, ta ci gaba da kasancewa babu tasirin ta’addancin Boko Haram a duk tsawon mulkin Gwamna Bala Mohammed.

 

“Wannan nasara ba ta zo haka nan ba. Ta samo asali ne daga manufofi na gangan, kyakkyawar haɗin gwiwa da hukumomin tsaro, da ƙudurin gwamna na hana ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka samun kafar zama a jihar,” sanarwar ta ƙara da cewa.

 

Ƙungiyar ta bayyana zarge-zargen da ke alaƙanta gwamnan da ɗaukar nauyin ta’addanci a matsayin zargin da hankali ba zai ɗauka ba lura da azamar gwamnan na kyautata harkokin tsaro, kuma zargin ya saɓanin haƙiƙankn abin da mutanen Jihar Bauchi shaidawa na samun ingancin tsaro da kwanciyar hankali a zahirance.

 

“Gwamna da ya dinga hana ‘yan ta’adda samun sarari, ya kare al’umma, kuma ya tabbatar da dorewar zaman lafiya ba za a iya kiran sa mai ɗaukar nauyin ta’addanci ba ta kowace hanya,” In ji su.

 

Baya ga tsaro, ‘yan majalisan su haskaka abin da suka kira manyan nasarori da ba a taɓa ganin irinsu ba a fannonin ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da walwalar jama’a a tsawon shekaru shida na mulkin Gwamna Bala Mohammed.

 

“Waɗannan nasarori sun fi kowace yekuwar siyasa, kuma suna bayyana ƙudurin gwamna na kyakkyawan shugabanci da mayar da hankali kan jin daɗin jama’a,” In ji sanarwar.

 

Ƙungiyar ‘yan majalisun PDP ta Bauchi ta yi kira ga ’yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu tare da yin nazari mai kyau, tana mai roƙon jama’a su mutunta doka da oda tare da barin gaskiya ta bayyana kanta ta hanyoyin da doka ta tanada.

 

“Muna da cikakken tabbacin cewa mutuncin Gwamna Bala Mohammed, tarihinsa na aiki da hidimarsa ga Jihar Bauchi za su tabbata a ƙarshe,” in ji sanarwar a ƙarshe.

PDP
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Ci Gaban Kirkire-kikiren Kasar Sin: Abin Da Wasu Manyan Jaridun Duniya Suka Fada

Ci Gaban Kirkire-kikiren Kasar Sin: Abin Da Wasu Manyan Jaridun Duniya Suka Fada

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.