ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisar PDP Sun Yi Allah-wadai Da Zargin Alaƙanta Gwamnan Bauchi Da Ɗaukar Nauyin Ta’addanci

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Bala Mohammed

’Yan Majalisar Wakilai na Jam’iyyar PDP daga Jihar Bauchi sun bayyana cikakken goyon baya da biyayya ba tare da tangarɗa ba ga Gwamna Bala Muhammad, bisa abin da suka kira “yaɓa masa zargin alaka da ɗaukan nauyin ayyukan ta’addanci”.

 

A cikin wata sanarwa da suka fitar ga manema labarai jiya a Bauchi, ƙungiyar ‘yan majalisan ta ce duk da cewa batun yana gaban kotu a halin yanzu, ya zama dole a tunatar da ‘yan Nijeriya tarihin Gwamna Bala Mohammed na bada fifiko da muhimmanta harkokin tsaro, kwanciyar hankali da ci gaban Jihar Bauchi a kowane lokaci.

ADVERTISEMENT
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙaƙaba Haraji Kan Ƙasashen Da Ke Kasuwanci Da Iran
  • AFCON 2025: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Karawar Nijeriya Da Morocco

“Yana da muhimmanci mu jaddada ingantaccen tarihi na Gwamna Bala Mohammed a matsayin shugaba da ya dinga sanya kwanciyar al’umma da tsaronsu da ci gaban Jihar Bauchi sama da komai,” In ji sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Sanarwar ta samu sa hannun ’yan Majalisar Wakilai na tarayya bakwai na PDP daga Jihar Bauchi da suka haɗa da Hon. Aliyu Aminu Garu (Mazaɓar Tarayya ta Bauchi), Hon. Mansur Manu Soro (Darazo/Ganjuwa), Hon. Auwalu Gwalabe (Katagum), Hon. Adamu Hashimu Ranga (Ningi/Warji), Hon. Mohammed Dan Abba Shehu (Zaki), Hon. Bappa Aliyu Misau (Misau/Dambam), da Hon. Sani Ibrahim Tanko (Da ke wakiltar Mazaɓar Shira/Giade).

 

A cewar ƙungiyar, Gwamna Bala Mohammed ya yi nasarar rage ayyukan ‘yan fashi da makami a Jihar Bauchi tsawon shekaru shida da suka gabata, duk da wata matsalar tsaro da ke tasowa sakamakon makwabtakar jihar da jihohin da ke fama da matsalar fashi da makami kamar Zamfara da Katsina.

 

“A daidai lokacin da matsalar tsaro ta tilasta wa jama’a yin ƙaura a Arewa maso Yamma da wasu sassan ƙasar nan, Jihar Bauchi ta ci gaba da kasancewa cikin aminci kuma wurin samun mafaka, sakamakon shugabanci mai inganci da hangen nesa da kuma shirin ko ta kwana ga matsalolin tsaro,” In ji su.

 

‘Yan Majalisar sun kuma jaddada cewa duk da kasancewar Jihar Bauchi a yankin Arewa Maso Gabas, ta ci gaba da kasancewa babu tasirin ta’addancin Boko Haram a duk tsawon mulkin Gwamna Bala Mohammed.

 

“Wannan nasara ba ta zo haka nan ba. Ta samo asali ne daga manufofi na gangan, kyakkyawar haɗin gwiwa da hukumomin tsaro, da ƙudurin gwamna na hana ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka samun kafar zama a jihar,” sanarwar ta ƙara da cewa.

 

Ƙungiyar ta bayyana zarge-zargen da ke alaƙanta gwamnan da ɗaukar nauyin ta’addanci a matsayin zargin da hankali ba zai ɗauka ba lura da azamar gwamnan na kyautata harkokin tsaro, kuma zargin ya saɓanin haƙiƙankn abin da mutanen Jihar Bauchi shaidawa na samun ingancin tsaro da kwanciyar hankali a zahirance.

 

“Gwamna da ya dinga hana ‘yan ta’adda samun sarari, ya kare al’umma, kuma ya tabbatar da dorewar zaman lafiya ba za a iya kiran sa mai ɗaukar nauyin ta’addanci ba ta kowace hanya,” In ji su.

 

Baya ga tsaro, ‘yan majalisan su haskaka abin da suka kira manyan nasarori da ba a taɓa ganin irinsu ba a fannonin ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da walwalar jama’a a tsawon shekaru shida na mulkin Gwamna Bala Mohammed.

 

“Waɗannan nasarori sun fi kowace yekuwar siyasa, kuma suna bayyana ƙudurin gwamna na kyakkyawan shugabanci da mayar da hankali kan jin daɗin jama’a,” In ji sanarwar.

 

Ƙungiyar ‘yan majalisun PDP ta Bauchi ta yi kira ga ’yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu tare da yin nazari mai kyau, tana mai roƙon jama’a su mutunta doka da oda tare da barin gaskiya ta bayyana kanta ta hanyoyin da doka ta tanada.

 

“Muna da cikakken tabbacin cewa mutuncin Gwamna Bala Mohammed, tarihinsa na aiki da hidimarsa ga Jihar Bauchi za su tabbata a ƙarshe,” in ji sanarwar a ƙarshe.

PDP
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
PDP
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
PDP
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Next Post
Ci Gaban Kirkire-kikiren Kasar Sin: Abin Da Wasu Manyan Jaridun Duniya Suka Fada

Ci Gaban Kirkire-kikiren Kasar Sin: Abin Da Wasu Manyan Jaridun Duniya Suka Fada

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
PDP

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
PDP

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
PDP

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.