Rundunar sojin Nijeriya ta ‘yan ta’adda sama da 150 ne suka miƙa wuya ga dakarun Operation Hadin Kai a yankin Arewa maso Gabas cikin mako guda.
Rundunar Haɗin Gwiwar ta ce wannan adadi ya ƙaru sosai idan aka kwatanta da makon da ya gabata, lokacin da sama da kwamandoji, mayaƙa da masu alaƙa da ƙungiyoyin ‘yan ta’adda 50 suka miƙa wuya.
Sojojin sun ce ci gaba da gudanar da ayyukan tattara bayanan sirri da kuma ƙara matsa wa ƙungiyoyin ‘yan ta’adda ne ya jawo ƙaruwar masu miƙa wuya.
Wasu daga cikin waɗanda suka miƙa wuyan sun kuma bayar da makamai da alburusai.
A cewar rundunar, ana tantancewa da rubuta bayanan duk waɗanda suka miƙa wuya bisa ƙa’idojin da aka tanada da kuma dokokin ƙasa.
Rundunar Operation Hadin Kai ta ce za ta ci gaba da ƙoƙarinta na ƙarfafa wa sauran ‘yan ta’adda gwiwa su miƙa wuya tare da karya lagom ƙungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin.














