• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Ta’adda Sun Kai Wa Sojoji Hari A Abuja

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
‘Yan Ta’adda Sun Kai Wa Sojoji Hari A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan ta’adda sun farmaki wasu sojoji da ke sintiri a kan hanyar Kubwa zuwa Bwari da ke birnin tarayya Abuja.

Wasu rahotannin sirri sun bayyana cewar ‘yan ta’addan na shirin kai hari makarantar koyon aikin lauya da ke Bwari da wasu cibiyoyin gwamnati a Abuja.

  • Rashin Tsaro: Haramta Acaba ‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Za Su Rasa Aikin Yi – ACOMORAN
  • Zamu Hukunta Duk Wanda Ba Musulmin Ba Da Ya Sake Keta Harami – Saudiyya

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce harin na nuni da cewa ‘yan ta’addan sun mamaye birnin tarayya amma hukumomi sun ce suna kokarin gano maharan.

A cewar daya daga cikin majiyoyin, wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun yi wa dakarun sojin da ke sintir a kan hanyar Kubwa zuwa Bwari kwanton bauna.

Ya kara da cewa sojoji uku daga cikin dakarun sun jikkata yayin harin kuma an kwashe su zuwa asibiti domin kula da lafiyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

“Harin da aka kai a yankin na Bwari ya nuna cewa a zahiri ‘yan ta’addan suna nan a wurin kuma akwai yiwuwa su kai farmaki makarantar koyon aikin lauya da ke Bwari kamar yadda aka ruwaito a baya,” inji majiyar.

Da aka tuntubi mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji, Birgediya-Janar, Godfrey Abakpa, ya tabbatar da harin, amma ya ce sun yi nasarar fatattakar su.

Ya kara da cewa an kwashe sojojin da suka jikkata zuwa asibiti kuma suna samun kulawa.

“An kai musu hari kuma an yi nasarar dakile harin. Muna da ‘yan tsiraru da suka samu raunuka amma an su kai asibiti domin ba su kulawa.

“A halin yanzu dakarunmu na bincike a yankin domin fatattakar ‘yan ta’addan da suka addabi yankin baki daya. Ana shawartar mazauna yankin su ci gaba da gudanar da sana’o’insu, su ci gaba da ba mu hadin kai ta hanyar ba mu bayanan da suka dace domin mu samu nasara gano wadanda suka kai hari,” inji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAbujaBwariDakarun SojiHariKubwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Gasar Bidiyo Ta Matasan Sin Da Afrika Ta “Great To Meet You”

Next Post

Gwamnatin Ce Ta Harzuka Wanda Suka Sace Mu, Suka Fara Dukanmu -Wanda Ya Kubuta

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

2 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

11 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

13 hours ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

16 hours ago
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

1 day ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Ce Ta Harzuka Wanda Suka Sace Mu, Suka Fara Dukanmu -Wanda Ya Kubuta

Gwamnatin Ce Ta Harzuka Wanda Suka Sace Mu, Suka Fara Dukanmu -Wanda Ya Kubuta

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.