ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Mutum 1,532 Bisa Zargin Aikata Laifuka Daban-daban A Bauchi 

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta kama a ƙalla mutane 1,532 bisa zarginsu da aikata laifukan daban-daban a sassan jihar a cikin shekarar 2025 da muka yi bankwana da ita. 

 

ADVERTISEMENT

Rundunar ta kuma amshi kesa-kesai har guda 881 a tsawon wannan lokacin, daga cikin wannan adadin kesa-kesai 880 ne ta gurfanar da su a gaban kotuna daban-daban.

  • Tinubu Ya Ƙudiri Aniyar Magance Ƙalubalen Nijeriya – Sanata Danbaba Dambuwa
  • Tinubu Ya Ƙudiri Aniyar Magance Ƙalubalen Nijeriya – Sanata Danbaba Dambuwa

A cewar ‘yansandan, sun samu nasara kan kesa-kesai 124 waɗanda kotuna suka yanke musu hukunci, yayin da 756 suke kan fuskantar Shari’a a halin yanzu, sai kuma kes guda ɗaya wanda suke kan gudanar da bincike a kansa.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

 

Wannan na ƙunshe ne a cikin sanarwar manema labarai da Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Nafiu Habib ya fitar a ranar Labara, dangane da nasarorin da hukumar ta cimma a cikin shekara guda a ƙarƙashin Kwamishina, CP Sani-Omolori Aliyu, kan yaƙi da masu aikata laifukan daban-daban a jihar.

 

SP Habib ya ce jerin nau’ikan masu laifukan da suka kama na nuni da irin azama da jajircewar hukumar ne wajen kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar a kowani lokacin.

 

Ya yi bayanin cewar an samu nasarorin ne bisa ayyukan sintiri, ayyukan tsaro, kai samame wuraren da aka gano ‘yan ta’adda na zaune, dukka da nufin tsarkake jihar daga ayyukan miyagu masu janyo ta’addanci.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa bisa ayyukan haɗin guiwa a tsakanin sauran hukumomin tsaro, jama’an jihar, masu ruwa da tsaki, ba su rahoto a kan lokaci suna daga cikin hanyoyin da suka taimaka wa hukumar wajen kyautata ayyukan tsaro a jihar.

 

Dangane da makaman da suka kamo kuwa, ya ce sun cafke bindiga ƙirar AK-47 guda 6, wata bindiga ƙirar gida AK-47, harbi-ka-noƙe guda 12, fistol ƙirar gida gida 7, wasu nau’ikan bindiga ƙirar gida gida 6, alburusai masu rai guda 352, jakar harsasai masu rai 16 da kuma magazines guda 7.

 

Kazalika motoci guda 5 da Babura 16 ne aka kamo a tsawon wannan lokacin.

 

Sauran kayayyakin da aka kwato sun haɗa da takardar kuɗi na N1,000 guda 220 da ake zargin jabun ne, dala guda 5 nau’in dala-100 da ake zargi na jabu ne, wayoyin hannu guda 42 da aka kwato a cikin gida da kuma na fashi da makami, da tufafi guda huɗu masu ɗauke da jini da kuma sanduna 21 da ke da alaƙa da zargin aikata laifin kisan kai.

 

Sauran sun haɗa da adduna 43, gatari 3, da wani gatari 1 da ke da alaƙa da kisan kai da ƙungiyar asiri.

 

An kwato kwamfutoci 4 a cikin kesa-kesan fashi da makami, wasu adadin tabar wiwi, Tramadol tablets, wayoyin wutar lantarki, da kuma Filaya (pliers) guda uku an gano su a cikin ayyukan da ake zargin ana lalata ƙadarorin mutane ne.

 

Har-ila-yau, rundunar ‘yansandan jihar ta kuma kwato shanu guda 12 a tsawon wannan lokaci.

 

A cewar rundunar a cikin shekara guda an ƙiyasce ƙadarorin da aka yi asararsu sun kai na Naira miliyan 129.8, yayin da kuma adadin ƙadarorin da aka samu nasarar kwatowa sun kai na Naira miliyan 54.2.

 

SP Nafiu Habib ya bada tabbacin cewar a shekarar 2026 rundunar za ta ƙada jan ɗamara domin yaƙi da masu aikata laifuka tare da tabbatar da inganta kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar. Sun kuma nemi ƙarin haɗin kan jama’an jihar domin cimma nasarorin ayyukan da suka sanya a gaba.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027
Manyan Labarai

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato
Manyan Labarai

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Next Post
Kakakin Babban Yankin Sin: Jawabin Jagoran Taiwan Lai Ching-Te Cike Yake Da Karairayi Da Nuna Kiyayya

Kakakin Babban Yankin Sin: Jawabin Jagoran Taiwan Lai Ching-Te Cike Yake Da Karairayi Da Nuna Kiyayya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.