ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Mutum 1,532 Bisa Zargin Aikata Laifuka Daban-daban A Bauchi 

by Leadership Hausa
7 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta kama a ƙalla mutane 1,532 bisa zarginsu da aikata laifukan daban-daban a sassan jihar a cikin shekarar 2025 da muka yi bankwana da ita. 

 

ADVERTISEMENT

Rundunar ta kuma amshi kesa-kesai har guda 881 a tsawon wannan lokacin, daga cikin wannan adadin kesa-kesai 880 ne ta gurfanar da su a gaban kotuna daban-daban.

  • Tinubu Ya Ƙudiri Aniyar Magance Ƙalubalen Nijeriya – Sanata Danbaba Dambuwa
  • Tinubu Ya Ƙudiri Aniyar Magance Ƙalubalen Nijeriya – Sanata Danbaba Dambuwa

A cewar ‘yansandan, sun samu nasara kan kesa-kesai 124 waɗanda kotuna suka yanke musu hukunci, yayin da 756 suke kan fuskantar Shari’a a halin yanzu, sai kuma kes guda ɗaya wanda suke kan gudanar da bincike a kansa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

 

Wannan na ƙunshe ne a cikin sanarwar manema labarai da Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Nafiu Habib ya fitar a ranar Labara, dangane da nasarorin da hukumar ta cimma a cikin shekara guda a ƙarƙashin Kwamishina, CP Sani-Omolori Aliyu, kan yaƙi da masu aikata laifukan daban-daban a jihar.

 

SP Habib ya ce jerin nau’ikan masu laifukan da suka kama na nuni da irin azama da jajircewar hukumar ne wajen kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar a kowani lokacin.

 

Ya yi bayanin cewar an samu nasarorin ne bisa ayyukan sintiri, ayyukan tsaro, kai samame wuraren da aka gano ‘yan ta’adda na zaune, dukka da nufin tsarkake jihar daga ayyukan miyagu masu janyo ta’addanci.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa bisa ayyukan haɗin guiwa a tsakanin sauran hukumomin tsaro, jama’an jihar, masu ruwa da tsaki, ba su rahoto a kan lokaci suna daga cikin hanyoyin da suka taimaka wa hukumar wajen kyautata ayyukan tsaro a jihar.

 

Dangane da makaman da suka kamo kuwa, ya ce sun cafke bindiga ƙirar AK-47 guda 6, wata bindiga ƙirar gida AK-47, harbi-ka-noƙe guda 12, fistol ƙirar gida gida 7, wasu nau’ikan bindiga ƙirar gida gida 6, alburusai masu rai guda 352, jakar harsasai masu rai 16 da kuma magazines guda 7.

 

Kazalika motoci guda 5 da Babura 16 ne aka kamo a tsawon wannan lokacin.

 

Sauran kayayyakin da aka kwato sun haɗa da takardar kuɗi na N1,000 guda 220 da ake zargin jabun ne, dala guda 5 nau’in dala-100 da ake zargi na jabu ne, wayoyin hannu guda 42 da aka kwato a cikin gida da kuma na fashi da makami, da tufafi guda huɗu masu ɗauke da jini da kuma sanduna 21 da ke da alaƙa da zargin aikata laifin kisan kai.

 

Sauran sun haɗa da adduna 43, gatari 3, da wani gatari 1 da ke da alaƙa da kisan kai da ƙungiyar asiri.

 

An kwato kwamfutoci 4 a cikin kesa-kesan fashi da makami, wasu adadin tabar wiwi, Tramadol tablets, wayoyin wutar lantarki, da kuma Filaya (pliers) guda uku an gano su a cikin ayyukan da ake zargin ana lalata ƙadarorin mutane ne.

 

Har-ila-yau, rundunar ‘yansandan jihar ta kuma kwato shanu guda 12 a tsawon wannan lokaci.

 

A cewar rundunar a cikin shekara guda an ƙiyasce ƙadarorin da aka yi asararsu sun kai na Naira miliyan 129.8, yayin da kuma adadin ƙadarorin da aka samu nasarar kwatowa sun kai na Naira miliyan 54.2.

 

SP Nafiu Habib ya bada tabbacin cewar a shekarar 2026 rundunar za ta ƙada jan ɗamara domin yaƙi da masu aikata laifuka tare da tabbatar da inganta kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar. Sun kuma nemi ƙarin haɗin kan jama’an jihar domin cimma nasarorin ayyukan da suka sanya a gaba.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Kakakin Babban Yankin Sin: Jawabin Jagoran Taiwan Lai Ching-Te Cike Yake Da Karairayi Da Nuna Kiyayya

Kakakin Babban Yankin Sin: Jawabin Jagoran Taiwan Lai Ching-Te Cike Yake Da Karairayi Da Nuna Kiyayya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.