ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Cin Namijin Goro Na Hana Maza Haihuwa

by Sani Anwar
6 months ago
Goro

Bincike ya tabbatar da cewa, muddin aka jima ana amfani da namijin goro; babu shakka hakan ka iya kawo barazana ga ƙwayoyin halittar da suke taimakawa wajen haihuwa. Ma’ana, rashin samun haihuwa.

Mutane da dama na amfani da namijin goro tare da sanya wa a ransu cewa, sakamakon sinadarin da namijin goron ke ɗauke da shi; zai iya taimaka wa maza wajen ɗanɗano ko gamsar da iyalansu yayin saduwar aure, wanda a gefe guda kuma yana barazana ga ƙwayoyin halittar da suke taimakawa wajen haihuwa.

  • Jagororin Kasar Sin Sun Halarci Bikin Gala Na Sabuwar Shekara Da Ya Kunshi Wasan Opera Na Gargajiya
  • Gwamnatin Katsina Ta Kare Shirinta Na Sakin Ƴan Ta’adda 70 Daga Gidan Yari

A dukkanin binciken da suka gabata, sun tabbatar da cewa; sinadarin namijin goro, ba ya ƙara wa ɗa namiji kuzari ko ƙarfin sha’awa ko kuma maganin mazakuta, hasali ma, daɗewa ana yin ta’ammali ko cin namijin goron ba bisa ƙa’ida ba, yana iya haifar wa da ɗa namiji matsalar rashin haihuwa.

ADVERTISEMENT

Haka nan, namijin goro yana ɗauke da sinadarin da ke taimakawa wajen narkar da abinci, yana kuma taimaka wa jikin mutum wajen fitar da ƙwayoyin cutar da jiki bai san su ba ko kuma waɗanda za su iya lalata garkuwar jiki.

Haka zalika, namijin goro, na da sinadarin da ke taimakawa wajen ganin jiki ya samu waraka a ɓangaren kumburi tare da rage yawan kitsen da ke tattare a jikin Ɗan’adam ya kuma sa kitsen ya ragu ya yi daidai wadaida a jikin mutum.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Bugu da ƙari, Namijin goro na ɗauke da sinadarin da ke maganin abubuwan da ke da alaƙa da Maleriya ko ciwon siga, wanda ka iya yin maganin zazzaɓin cizon sauro, inda a wani ɓangaren ma ake ganin kamar ya fi alfanu ga masu ciwon siga; ta hanyar daidaita sigan, musamman idan ya yi yawa a jikin mutum.

Har ila yau, namijin goro na ɗauke da sinadarin da ke bunƙasa garkuwar jiki, ma’ana yana da abin da ake kira a turance ‘antioɗidant’. A taƙaice, namijin goro na ɗauke da sinadarin da zai iya tallafa wa jikin Ɗan’adam, ya fitar da abin da ka’iya zama guba ko wani abu makamancin haka a jikinsa.

Kazalika, namijin goro yana taimaka wa garkuwar jikin Ɗan’adam, musamman wajen buɗe ƙofofin huhu, hanyoyin iska; wanda Ɗan’adam, galibi mai fama da matsalar cutar asma ko fitar da numfashi, kan iya samun waraka idan ya yi amfani da shi.

Don haka, a nan yana da kyau a fahimci cewa; Namijin goro na da matuƙar muhimmanci ga lafiyar Ɗan’adam, amma a gefe guda kuma idan ya yi yawa, ma’ana; idan aka fiye amfani da shi, ta hanyar cin sa a kullum, musamman maza za su iya fuskantar matsalar rashin haihuwa.

Mun ɗauko wannan ne daga daga tattaunawar da BBC ta yi da Dakta Auwal Musa Umar

 

Goro
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Sirrin Kasar Sin Na Fitar Da Al’ummunta Daga Kangin Talauci

Sirrin Kasar Sin Na Fitar Da Al’ummunta Daga Kangin Talauci

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.