ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Cin Namijin Goro Na Hana Maza Haihuwa

by Sani Anwar
5 months ago
Goro

Bincike ya tabbatar da cewa, muddin aka jima ana amfani da namijin goro; babu shakka hakan ka iya kawo barazana ga ƙwayoyin halittar da suke taimakawa wajen haihuwa. Ma’ana, rashin samun haihuwa.

Mutane da dama na amfani da namijin goro tare da sanya wa a ransu cewa, sakamakon sinadarin da namijin goron ke ɗauke da shi; zai iya taimaka wa maza wajen ɗanɗano ko gamsar da iyalansu yayin saduwar aure, wanda a gefe guda kuma yana barazana ga ƙwayoyin halittar da suke taimakawa wajen haihuwa.

  • Jagororin Kasar Sin Sun Halarci Bikin Gala Na Sabuwar Shekara Da Ya Kunshi Wasan Opera Na Gargajiya
  • Gwamnatin Katsina Ta Kare Shirinta Na Sakin Ƴan Ta’adda 70 Daga Gidan Yari

A dukkanin binciken da suka gabata, sun tabbatar da cewa; sinadarin namijin goro, ba ya ƙara wa ɗa namiji kuzari ko ƙarfin sha’awa ko kuma maganin mazakuta, hasali ma, daɗewa ana yin ta’ammali ko cin namijin goron ba bisa ƙa’ida ba, yana iya haifar wa da ɗa namiji matsalar rashin haihuwa.

ADVERTISEMENT

Haka nan, namijin goro yana ɗauke da sinadarin da ke taimakawa wajen narkar da abinci, yana kuma taimaka wa jikin mutum wajen fitar da ƙwayoyin cutar da jiki bai san su ba ko kuma waɗanda za su iya lalata garkuwar jiki.

Haka zalika, namijin goro, na da sinadarin da ke taimakawa wajen ganin jiki ya samu waraka a ɓangaren kumburi tare da rage yawan kitsen da ke tattare a jikin Ɗan’adam ya kuma sa kitsen ya ragu ya yi daidai wadaida a jikin mutum.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Bugu da ƙari, Namijin goro na ɗauke da sinadarin da ke maganin abubuwan da ke da alaƙa da Maleriya ko ciwon siga, wanda ka iya yin maganin zazzaɓin cizon sauro, inda a wani ɓangaren ma ake ganin kamar ya fi alfanu ga masu ciwon siga; ta hanyar daidaita sigan, musamman idan ya yi yawa a jikin mutum.

Har ila yau, namijin goro na ɗauke da sinadarin da ke bunƙasa garkuwar jiki, ma’ana yana da abin da ake kira a turance ‘antioɗidant’. A taƙaice, namijin goro na ɗauke da sinadarin da zai iya tallafa wa jikin Ɗan’adam, ya fitar da abin da ka’iya zama guba ko wani abu makamancin haka a jikinsa.

Kazalika, namijin goro yana taimaka wa garkuwar jikin Ɗan’adam, musamman wajen buɗe ƙofofin huhu, hanyoyin iska; wanda Ɗan’adam, galibi mai fama da matsalar cutar asma ko fitar da numfashi, kan iya samun waraka idan ya yi amfani da shi.

Don haka, a nan yana da kyau a fahimci cewa; Namijin goro na da matuƙar muhimmanci ga lafiyar Ɗan’adam, amma a gefe guda kuma idan ya yi yawa, ma’ana; idan aka fiye amfani da shi, ta hanyar cin sa a kullum, musamman maza za su iya fuskantar matsalar rashin haihuwa.

Mun ɗauko wannan ne daga daga tattaunawar da BBC ta yi da Dakta Auwal Musa Umar

 

Goro
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Sirrin Kasar Sin Na Fitar Da Al’ummunta Daga Kangin Talauci

Sirrin Kasar Sin Na Fitar Da Al’ummunta Daga Kangin Talauci

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.