ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Shiga Hannu Bisa Zargin Fashi Da Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Jigawa

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Mutum

Rundunar Ƴansandan Jihar Jigawa ta kama mutum 10 da ake zargin suna da hannu a ayyukan fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, da sauran laifuka a faɗin jihar.

Jaridar PUNCH Metro ta samu labarin cewa, a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Shi’isu Adam, ya fitar ga manema labarai a ranar Litinin, an bayyana cewa aikin, wanda aka gudanar a lokaci guda a sassa daban-daban na jihar, ya kai ga kama wani wanda ake nema saboda fashi da makami da wasu mutum tara, tare da ƙwato miyagun ƙwayoyi guda 7,028, ciki har da sinadarin roba, da ganyayyaki busassu da ake zargin su ne ganyen hemp na Indiya (Indian hemp).

  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
  • CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

Adam ya ƙara da cewa, an kama mutum bakwai da ake zargin masu safarar miyagun ƙwayoyi ne ko masu amfani da su. Sun haɗa da: Nadabo Ibrahim (25) daga Kwanar Garki; Alkassaim Sa’idu (27) daga ƙauyen Acauya, Ƙaramar Hukumar Sule Tankarkar; Ibrahim Sambo (22) daga Bitinariya Ƙuarters, Hadejia LGA; Usman Abubakar (30) daga Dunari Ƙuarters; Aminu Muhd (25) daga Dunari Ƙuarters; Yusuf Sale (22) daga Nassarawa Ƙuarters; da Ibrahim Ismail (23) daga Marakawa Ƙuarters, Ringim LGA.

ADVERTISEMENT

Ya ce jami’an ƴansanda daga sashen B, Hadejia, sun kuma ƙwato babur mai launin fari na Jincheng wanda aka ruwaito an sace shi daga gidan wani mai ƙorafi a Rinde Ƙuarters, garin Hadejia.

“An ci gaba da ƙoƙarin gano wanda ya aikata sata ko waɗanda ke da hannu a ciki, yayin da aka mayar da babur ɗin ga sahihin mai shi a kan belin,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

A wani aiki daban, Adam ya ce jami’an sashen Malam-Madori sun samu shanu guda biyu da ake zargin an sace su a gefen Dunari Ƙuarters.

“Waɗanda ake zargin sun bar shanun suka tsere zuwa cikin wani daji dake kusa,” ya ƙara da cewa.

Ya bayyana cewa an ƙara himma wajen gano sahihin mai shanun, kama waɗanda ke da hannu a satar, da rage laifukan satar shanu a yankin.

Rundunar ta ƙara da cewa an kama Shu’aibu Musa, wanda ake nema saboda fashi da makami, saboda satar rakumi, inda aka ƙwato raƙumi da aka sace daga gare shi.

Adam ya ce Musa an miƙa shi zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar a Dutse domin cikakken bincike da gurfanarwa a gaban shari’a.

A wani lamari makamancin haka, ƴan sanda sun kama wani da ake zargin mai satar wayoyi, Abdullahi Isyaku (20), da kuma wanda ya karɓi wayoyin sata, Nasir Saleh (30), a garin Sundimina.

“Ƴan zargin sun sace waya guda Infiniɗ Smart 10, Tecno Camon 19, waya mai maballin Itel, da kuɗi Naira 20,000. An sayar da wayoyin ne kan Naira 61,000. An gurfanar da su a gaban kotu, kuma bincike ya kammala,” in ji Adam.

Kakakin rundunar ya ƙara da cewa, haɗin kai daga jama’a ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci yana da matuƙar muhimmanci a yaki da laifuka, inda ya yi kira ga mazauna jihar da su ƙara ƙoƙarin bayar da bayanai domin taimaka wa ƴansanda.

“Ana ci gaba da ƙoƙarin kamo wanda ake zargin ko waɗanda ke da hannu a satar, yayin da aka mayar da babur ɗin da aka ƙwato ga asalin mai shi a kan beli,” in ji shi.

A wani aiki daban, Adam ya ce jami’an sashen Malam-Madori sun samu shanu guda biyu da ake zargin an sace su a gefen Unguwar Dunari.

“Waɗanda ake zargin sun bar shanun suka tsere zuwa cikin wani daji dake kusa,” ya ƙara da cewa.

Mutum
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da 'Ya'yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.