ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Shiga Hannu Bisa Zargin Fashi Da Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Jigawa

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Mutum

Rundunar Ƴansandan Jihar Jigawa ta kama mutum 10 da ake zargin suna da hannu a ayyukan fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, da sauran laifuka a faɗin jihar.

Jaridar PUNCH Metro ta samu labarin cewa, a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Shi’isu Adam, ya fitar ga manema labarai a ranar Litinin, an bayyana cewa aikin, wanda aka gudanar a lokaci guda a sassa daban-daban na jihar, ya kai ga kama wani wanda ake nema saboda fashi da makami da wasu mutum tara, tare da ƙwato miyagun ƙwayoyi guda 7,028, ciki har da sinadarin roba, da ganyayyaki busassu da ake zargin su ne ganyen hemp na Indiya (Indian hemp).

  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
  • CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

Adam ya ƙara da cewa, an kama mutum bakwai da ake zargin masu safarar miyagun ƙwayoyi ne ko masu amfani da su. Sun haɗa da: Nadabo Ibrahim (25) daga Kwanar Garki; Alkassaim Sa’idu (27) daga ƙauyen Acauya, Ƙaramar Hukumar Sule Tankarkar; Ibrahim Sambo (22) daga Bitinariya Ƙuarters, Hadejia LGA; Usman Abubakar (30) daga Dunari Ƙuarters; Aminu Muhd (25) daga Dunari Ƙuarters; Yusuf Sale (22) daga Nassarawa Ƙuarters; da Ibrahim Ismail (23) daga Marakawa Ƙuarters, Ringim LGA.

ADVERTISEMENT

Ya ce jami’an ƴansanda daga sashen B, Hadejia, sun kuma ƙwato babur mai launin fari na Jincheng wanda aka ruwaito an sace shi daga gidan wani mai ƙorafi a Rinde Ƙuarters, garin Hadejia.

“An ci gaba da ƙoƙarin gano wanda ya aikata sata ko waɗanda ke da hannu a ciki, yayin da aka mayar da babur ɗin ga sahihin mai shi a kan belin,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

A wani aiki daban, Adam ya ce jami’an sashen Malam-Madori sun samu shanu guda biyu da ake zargin an sace su a gefen Dunari Ƙuarters.

“Waɗanda ake zargin sun bar shanun suka tsere zuwa cikin wani daji dake kusa,” ya ƙara da cewa.

Ya bayyana cewa an ƙara himma wajen gano sahihin mai shanun, kama waɗanda ke da hannu a satar, da rage laifukan satar shanu a yankin.

Rundunar ta ƙara da cewa an kama Shu’aibu Musa, wanda ake nema saboda fashi da makami, saboda satar rakumi, inda aka ƙwato raƙumi da aka sace daga gare shi.

Adam ya ce Musa an miƙa shi zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar a Dutse domin cikakken bincike da gurfanarwa a gaban shari’a.

A wani lamari makamancin haka, ƴan sanda sun kama wani da ake zargin mai satar wayoyi, Abdullahi Isyaku (20), da kuma wanda ya karɓi wayoyin sata, Nasir Saleh (30), a garin Sundimina.

“Ƴan zargin sun sace waya guda Infiniɗ Smart 10, Tecno Camon 19, waya mai maballin Itel, da kuɗi Naira 20,000. An sayar da wayoyin ne kan Naira 61,000. An gurfanar da su a gaban kotu, kuma bincike ya kammala,” in ji Adam.

Kakakin rundunar ya ƙara da cewa, haɗin kai daga jama’a ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci yana da matuƙar muhimmanci a yaki da laifuka, inda ya yi kira ga mazauna jihar da su ƙara ƙoƙarin bayar da bayanai domin taimaka wa ƴansanda.

“Ana ci gaba da ƙoƙarin kamo wanda ake zargin ko waɗanda ke da hannu a satar, yayin da aka mayar da babur ɗin da aka ƙwato ga asalin mai shi a kan beli,” in ji shi.

A wani aiki daban, Adam ya ce jami’an sashen Malam-Madori sun samu shanu guda biyu da ake zargin an sace su a gefen Unguwar Dunari.

“Waɗanda ake zargin sun bar shanun suka tsere zuwa cikin wani daji dake kusa,” ya ƙara da cewa.

Mutum
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da 'Ya'yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.