ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Shiga Hannu Bisa Zargin Fashi Da Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Jigawa

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Mutum

Rundunar Ƴansandan Jihar Jigawa ta kama mutum 10 da ake zargin suna da hannu a ayyukan fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, da sauran laifuka a faɗin jihar.

Jaridar PUNCH Metro ta samu labarin cewa, a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Shi’isu Adam, ya fitar ga manema labarai a ranar Litinin, an bayyana cewa aikin, wanda aka gudanar a lokaci guda a sassa daban-daban na jihar, ya kai ga kama wani wanda ake nema saboda fashi da makami da wasu mutum tara, tare da ƙwato miyagun ƙwayoyi guda 7,028, ciki har da sinadarin roba, da ganyayyaki busassu da ake zargin su ne ganyen hemp na Indiya (Indian hemp).

  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
  • CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

Adam ya ƙara da cewa, an kama mutum bakwai da ake zargin masu safarar miyagun ƙwayoyi ne ko masu amfani da su. Sun haɗa da: Nadabo Ibrahim (25) daga Kwanar Garki; Alkassaim Sa’idu (27) daga ƙauyen Acauya, Ƙaramar Hukumar Sule Tankarkar; Ibrahim Sambo (22) daga Bitinariya Ƙuarters, Hadejia LGA; Usman Abubakar (30) daga Dunari Ƙuarters; Aminu Muhd (25) daga Dunari Ƙuarters; Yusuf Sale (22) daga Nassarawa Ƙuarters; da Ibrahim Ismail (23) daga Marakawa Ƙuarters, Ringim LGA.

ADVERTISEMENT

Ya ce jami’an ƴansanda daga sashen B, Hadejia, sun kuma ƙwato babur mai launin fari na Jincheng wanda aka ruwaito an sace shi daga gidan wani mai ƙorafi a Rinde Ƙuarters, garin Hadejia.

“An ci gaba da ƙoƙarin gano wanda ya aikata sata ko waɗanda ke da hannu a ciki, yayin da aka mayar da babur ɗin ga sahihin mai shi a kan belin,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

A wani aiki daban, Adam ya ce jami’an sashen Malam-Madori sun samu shanu guda biyu da ake zargin an sace su a gefen Dunari Ƙuarters.

“Waɗanda ake zargin sun bar shanun suka tsere zuwa cikin wani daji dake kusa,” ya ƙara da cewa.

Ya bayyana cewa an ƙara himma wajen gano sahihin mai shanun, kama waɗanda ke da hannu a satar, da rage laifukan satar shanu a yankin.

Rundunar ta ƙara da cewa an kama Shu’aibu Musa, wanda ake nema saboda fashi da makami, saboda satar rakumi, inda aka ƙwato raƙumi da aka sace daga gare shi.

Adam ya ce Musa an miƙa shi zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar a Dutse domin cikakken bincike da gurfanarwa a gaban shari’a.

A wani lamari makamancin haka, ƴan sanda sun kama wani da ake zargin mai satar wayoyi, Abdullahi Isyaku (20), da kuma wanda ya karɓi wayoyin sata, Nasir Saleh (30), a garin Sundimina.

“Ƴan zargin sun sace waya guda Infiniɗ Smart 10, Tecno Camon 19, waya mai maballin Itel, da kuɗi Naira 20,000. An sayar da wayoyin ne kan Naira 61,000. An gurfanar da su a gaban kotu, kuma bincike ya kammala,” in ji Adam.

Kakakin rundunar ya ƙara da cewa, haɗin kai daga jama’a ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci yana da matuƙar muhimmanci a yaki da laifuka, inda ya yi kira ga mazauna jihar da su ƙara ƙoƙarin bayar da bayanai domin taimaka wa ƴansanda.

“Ana ci gaba da ƙoƙarin kamo wanda ake zargin ko waɗanda ke da hannu a satar, yayin da aka mayar da babur ɗin da aka ƙwato ga asalin mai shi a kan beli,” in ji shi.

A wani aiki daban, Adam ya ce jami’an sashen Malam-Madori sun samu shanu guda biyu da ake zargin an sace su a gefen Unguwar Dunari.

“Waɗanda ake zargin sun bar shanun suka tsere zuwa cikin wani daji dake kusa,” ya ƙara da cewa.

Mutum
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da 'Ya'yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.