ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Yahaya Ya Yi Maraba Da Ƴan Majalisa 2 Na PDP Da Suka Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
5 months ago
PDP

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karɓi ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe biyu waɗanda suka sauya sheƙa daga Jam’iyyar PDP zuwa Jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara ƙarfafa ikon jam’iyyar mai mulki a majalisar.

Ƴan majalisan su ne Hon. Gabriel Galadima Fushison, mai wakiltar Mazaɓar Kaltungo ta Yamma da kuma Hon. Malon Nimrod Yari, mai wakiltar Mazaɓar Billiri ta Yamma. Da wannan sabon ci gaba, APC yanzu tana da kujeru 23 cikin 24 a Majalisar Dokokin Jihar Gombe.

  • Ban Ce Ba Zan Shiga APC Ba, Amma Dole A Kafa Sharuɗɗa – Kwankwaso 
  • Ɗan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Koma APC

Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abubakar Mohammed Luggerewo, tare da Mataimakinsa, Hon. Sadam Bello da sauran manyan jami’an majalisar ne suka jagorance su zuwa ofishin Gwamnan.

ADVERTISEMENT

Ƴan majalisan da suka sauya sheƙa suka ce shawarar da suka yanken ta samo asali ne daga salon mulkin Gwamna Inuwa Yahaya na haɗa kan jama’a, da jagoranci mai kyau da kuma kyawawan ayyukan da yake gudanarwa a faɗin jihar.

Suka ce ko da a lokacin da suke adawa, ba a taɓa nuna musu wariya saboda bambancin jam’iyya ba, suna masu cewa al’ummomin mazaɓunsu sun amfana sosai daga ayyukan gwamnati na romon demokraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A cewarsu, adalcin Gwamnan, da sauƙin kansa wajen mu’amala da jama’a da kuma jajircewarsa wajen samar da ci gaba cikin adalci ne suka gamsar da su cewa hanya mafi kyau ta sakanta irin wannan karamci ita ce su haɗa hannu da shi wajen ciyar da Jihar Gombe gaba.

Da ya ke maraba da ƴan majalisan zuwa cikin Jam’iyyar APC, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana sauya sheƙar tasu a matsayin wata ƙuri’ar amincewa da gwamnatinsa da manufofinta na kyautatawa al’umma.

Ya tabbatar musu cewa za a yi musu adalci da daidaito, kuma za a dama dasu yadda ya kamata a cikin jam’iyyar, yana mai jaddada cewa APC jam’iyya ce ta haɗin kai, ci gaba da kuma yi wa jama’a hidima.

Gwamnan ya kuma yabawa shugabanni da ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe saboda ci gaba da haɗin gwiwar da suke yi da ɓangaren zartarwa, yana mai bayyana kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin ɓangarorin gwamnatin biyu a matsayin muhimmiya wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban da jihar ke samu a halin yanzu.

Gwamna Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa bisa ci gaba da samun haɗin kai a cikin jam’iyyar, APC za ta samu gagarumar nasara a babban zaɓen 2027, ba kawai a Jihar Gombe ba har ma a faɗin ƙasa baki ɗaya.

Ismaila Uba Misilli, babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe da ya ke ƙarin haKe kan wannan matakin, ya ce idan dai za a iya tunawa, a farkon shekarar data gabata ma Hon. Zubairu Ayala, shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na’urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na'urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.