ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Yahaya Ya Yi Maraba Da Ƴan Majalisa 2 Na PDP Da Suka Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
5 months ago
PDP

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karɓi ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe biyu waɗanda suka sauya sheƙa daga Jam’iyyar PDP zuwa Jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara ƙarfafa ikon jam’iyyar mai mulki a majalisar.

Ƴan majalisan su ne Hon. Gabriel Galadima Fushison, mai wakiltar Mazaɓar Kaltungo ta Yamma da kuma Hon. Malon Nimrod Yari, mai wakiltar Mazaɓar Billiri ta Yamma. Da wannan sabon ci gaba, APC yanzu tana da kujeru 23 cikin 24 a Majalisar Dokokin Jihar Gombe.

  • Ban Ce Ba Zan Shiga APC Ba, Amma Dole A Kafa Sharuɗɗa – Kwankwaso 
  • Ɗan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Koma APC

Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abubakar Mohammed Luggerewo, tare da Mataimakinsa, Hon. Sadam Bello da sauran manyan jami’an majalisar ne suka jagorance su zuwa ofishin Gwamnan.

ADVERTISEMENT

Ƴan majalisan da suka sauya sheƙa suka ce shawarar da suka yanken ta samo asali ne daga salon mulkin Gwamna Inuwa Yahaya na haɗa kan jama’a, da jagoranci mai kyau da kuma kyawawan ayyukan da yake gudanarwa a faɗin jihar.

Suka ce ko da a lokacin da suke adawa, ba a taɓa nuna musu wariya saboda bambancin jam’iyya ba, suna masu cewa al’ummomin mazaɓunsu sun amfana sosai daga ayyukan gwamnati na romon demokraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A cewarsu, adalcin Gwamnan, da sauƙin kansa wajen mu’amala da jama’a da kuma jajircewarsa wajen samar da ci gaba cikin adalci ne suka gamsar da su cewa hanya mafi kyau ta sakanta irin wannan karamci ita ce su haɗa hannu da shi wajen ciyar da Jihar Gombe gaba.

Da ya ke maraba da ƴan majalisan zuwa cikin Jam’iyyar APC, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana sauya sheƙar tasu a matsayin wata ƙuri’ar amincewa da gwamnatinsa da manufofinta na kyautatawa al’umma.

Ya tabbatar musu cewa za a yi musu adalci da daidaito, kuma za a dama dasu yadda ya kamata a cikin jam’iyyar, yana mai jaddada cewa APC jam’iyya ce ta haɗin kai, ci gaba da kuma yi wa jama’a hidima.

Gwamnan ya kuma yabawa shugabanni da ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe saboda ci gaba da haɗin gwiwar da suke yi da ɓangaren zartarwa, yana mai bayyana kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin ɓangarorin gwamnatin biyu a matsayin muhimmiya wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban da jihar ke samu a halin yanzu.

Gwamna Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa bisa ci gaba da samun haɗin kai a cikin jam’iyyar, APC za ta samu gagarumar nasara a babban zaɓen 2027, ba kawai a Jihar Gombe ba har ma a faɗin ƙasa baki ɗaya.

Ismaila Uba Misilli, babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe da ya ke ƙarin haKe kan wannan matakin, ya ce idan dai za a iya tunawa, a farkon shekarar data gabata ma Hon. Zubairu Ayala, shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na’urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na'urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.