ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Yahaya Ya Yi Maraba Da Ƴan Majalisa 2 Na PDP Da Suka Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
6 months ago
PDP

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karɓi ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe biyu waɗanda suka sauya sheƙa daga Jam’iyyar PDP zuwa Jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara ƙarfafa ikon jam’iyyar mai mulki a majalisar.

Ƴan majalisan su ne Hon. Gabriel Galadima Fushison, mai wakiltar Mazaɓar Kaltungo ta Yamma da kuma Hon. Malon Nimrod Yari, mai wakiltar Mazaɓar Billiri ta Yamma. Da wannan sabon ci gaba, APC yanzu tana da kujeru 23 cikin 24 a Majalisar Dokokin Jihar Gombe.

  • Ban Ce Ba Zan Shiga APC Ba, Amma Dole A Kafa Sharuɗɗa – Kwankwaso 
  • Ɗan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Koma APC

Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abubakar Mohammed Luggerewo, tare da Mataimakinsa, Hon. Sadam Bello da sauran manyan jami’an majalisar ne suka jagorance su zuwa ofishin Gwamnan.

ADVERTISEMENT

Ƴan majalisan da suka sauya sheƙa suka ce shawarar da suka yanken ta samo asali ne daga salon mulkin Gwamna Inuwa Yahaya na haɗa kan jama’a, da jagoranci mai kyau da kuma kyawawan ayyukan da yake gudanarwa a faɗin jihar.

Suka ce ko da a lokacin da suke adawa, ba a taɓa nuna musu wariya saboda bambancin jam’iyya ba, suna masu cewa al’ummomin mazaɓunsu sun amfana sosai daga ayyukan gwamnati na romon demokraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

A cewarsu, adalcin Gwamnan, da sauƙin kansa wajen mu’amala da jama’a da kuma jajircewarsa wajen samar da ci gaba cikin adalci ne suka gamsar da su cewa hanya mafi kyau ta sakanta irin wannan karamci ita ce su haɗa hannu da shi wajen ciyar da Jihar Gombe gaba.

Da ya ke maraba da ƴan majalisan zuwa cikin Jam’iyyar APC, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana sauya sheƙar tasu a matsayin wata ƙuri’ar amincewa da gwamnatinsa da manufofinta na kyautatawa al’umma.

Ya tabbatar musu cewa za a yi musu adalci da daidaito, kuma za a dama dasu yadda ya kamata a cikin jam’iyyar, yana mai jaddada cewa APC jam’iyya ce ta haɗin kai, ci gaba da kuma yi wa jama’a hidima.

Gwamnan ya kuma yabawa shugabanni da ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe saboda ci gaba da haɗin gwiwar da suke yi da ɓangaren zartarwa, yana mai bayyana kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin ɓangarorin gwamnatin biyu a matsayin muhimmiya wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban da jihar ke samu a halin yanzu.

Gwamna Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa bisa ci gaba da samun haɗin kai a cikin jam’iyyar, APC za ta samu gagarumar nasara a babban zaɓen 2027, ba kawai a Jihar Gombe ba har ma a faɗin ƙasa baki ɗaya.

Ismaila Uba Misilli, babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe da ya ke ƙarin haKe kan wannan matakin, ya ce idan dai za a iya tunawa, a farkon shekarar data gabata ma Hon. Zubairu Ayala, shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na’urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na'urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.