ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Yahaya Ya Yi Maraba Da Ƴan Majalisa 2 Na PDP Da Suka Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
8 months ago
PDP

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karɓi ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe biyu waɗanda suka sauya sheƙa daga Jam’iyyar PDP zuwa Jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara ƙarfafa ikon jam’iyyar mai mulki a majalisar.

Ƴan majalisan su ne Hon. Gabriel Galadima Fushison, mai wakiltar Mazaɓar Kaltungo ta Yamma da kuma Hon. Malon Nimrod Yari, mai wakiltar Mazaɓar Billiri ta Yamma. Da wannan sabon ci gaba, APC yanzu tana da kujeru 23 cikin 24 a Majalisar Dokokin Jihar Gombe.

  • Ban Ce Ba Zan Shiga APC Ba, Amma Dole A Kafa Sharuɗɗa – Kwankwaso 
  • Ɗan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Koma APC

Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abubakar Mohammed Luggerewo, tare da Mataimakinsa, Hon. Sadam Bello da sauran manyan jami’an majalisar ne suka jagorance su zuwa ofishin Gwamnan.

ADVERTISEMENT

Ƴan majalisan da suka sauya sheƙa suka ce shawarar da suka yanken ta samo asali ne daga salon mulkin Gwamna Inuwa Yahaya na haɗa kan jama’a, da jagoranci mai kyau da kuma kyawawan ayyukan da yake gudanarwa a faɗin jihar.

Suka ce ko da a lokacin da suke adawa, ba a taɓa nuna musu wariya saboda bambancin jam’iyya ba, suna masu cewa al’ummomin mazaɓunsu sun amfana sosai daga ayyukan gwamnati na romon demokraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cewarsu, adalcin Gwamnan, da sauƙin kansa wajen mu’amala da jama’a da kuma jajircewarsa wajen samar da ci gaba cikin adalci ne suka gamsar da su cewa hanya mafi kyau ta sakanta irin wannan karamci ita ce su haɗa hannu da shi wajen ciyar da Jihar Gombe gaba.

Da ya ke maraba da ƴan majalisan zuwa cikin Jam’iyyar APC, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana sauya sheƙar tasu a matsayin wata ƙuri’ar amincewa da gwamnatinsa da manufofinta na kyautatawa al’umma.

Ya tabbatar musu cewa za a yi musu adalci da daidaito, kuma za a dama dasu yadda ya kamata a cikin jam’iyyar, yana mai jaddada cewa APC jam’iyya ce ta haɗin kai, ci gaba da kuma yi wa jama’a hidima.

Gwamnan ya kuma yabawa shugabanni da ƴan Majalisan Dokokin Jihar Gombe saboda ci gaba da haɗin gwiwar da suke yi da ɓangaren zartarwa, yana mai bayyana kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin ɓangarorin gwamnatin biyu a matsayin muhimmiya wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban da jihar ke samu a halin yanzu.

Gwamna Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa bisa ci gaba da samun haɗin kai a cikin jam’iyyar, APC za ta samu gagarumar nasara a babban zaɓen 2027, ba kawai a Jihar Gombe ba har ma a faɗin ƙasa baki ɗaya.

Ismaila Uba Misilli, babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe da ya ke ƙarin haKe kan wannan matakin, ya ce idan dai za a iya tunawa, a farkon shekarar data gabata ma Hon. Zubairu Ayala, shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na’urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

KASTLEA Ta Yaba Wa Gwamna Uba Sani Kan Samar Da Na'urorin Zamani Don Daƙile Haɗurra

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.