Wasu ’yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai hari wani masaukin ɗaliban Jami’ar Nasarawa da ke karatu a sashen Faculty of Engineering a garin Gudi.
An ce maharan sun kutsa cikin masaukin ɗaliban da ke yankin Ninzo a daren ranar Laraba, lamarin da ya tayar da hankalin mazauna yankin tare da hana mutane barci.
Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru ne a ranar Laraba, 6 ga watan Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 9 na dare.
Rundunar ’yansandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da ta aikewa manema labarai.
’Yansandan sun bayyana cewa maharan sun yi awon gaba da mutum bakwai, ciki har da ɗalibai shida.
An ce ɗaya daga cikin waɗanda aka sace ya kai ziyara ne lokacin da lamarin ya faru.
Kwamishinan ’Yansandan Jihar Nasarawa, CP Shattima Jauro Mohammed, ya kai ziyara wurin da abin ya faru domin duba halin da ake ciki.
Ya kuma tabbatar wa ɗalibai da mazauna yankin cewa rundunar za ta yi duk mai yiwuwa domin ceto waɗanda aka sace cikin ƙoshin lafiya.
Domin ƙarfafa aikin ceto, kwamishinan ya tura Area Commander na Akwanga domin jagorantar ayyukan sintiri da bincike a yankin har sai an ceto mutanen da aka sace.
Haka kuma, an tura haɗaɗɗiyar tawagar jami’an tsaro da suka haɗa da ’yansanda, DSS, sojoji, NSCDC da ƙungiyoyin sa-kai domin ƙara ƙaimi wajen gano maharan.
Rundunar ta buƙaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da duk wani bayani da zai taimaka wa jami’an tsaro wajen gudanar da bincike da ceto waɗanda aka sace.















Discussion about this post