June 12: Tinubu Ya Kafa Sabuwar Jami’a A Kaduna, Ya Karrama Marigayi Janar Yar’Adua
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa sabuwar jami’a a Jihar Kaduna tare da sanyawa jami’ar sunan marigayi Janar Shehu Musa Yar’Adua, a wani ɓangare na bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026.
Jami’ar za ta kasance da sunan janar Shehu Musa Yar’Adua University of Geological Sciences and Engineering Technology.
Tinubu ya bayyana hakan ne yayin jawabin Ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, inda ya ce an sauya sunan Institute of Petroleum Studies, Kaduna domin girmama gudunmawar marigayin wajen gwagwarmayar dimokuraɗiyya da kuma hangen nesansa na haɗin kan kasa.
Shugaban ya kuma karrama sauran jaruman gwagwarmayar June 12, yana mai cewa Nijeriya na bin bashin godiya ga waɗanda suka sha tsangwama, da zaman kurkuku da gudun hijira domin tabbatar da dimokuraɗiyya. Haka kuma ya sanar da bayar da lambobin yabo ga masu fafutukar dimokuraɗiyya da dama.
Tinubu ya jaddada cewa bayan shekaru 27 na mulkin farar hula ba tare da tangarɗa ba, lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su ƙara ƙarfafa cibiyoyin dimokuraɗiyya tare da tabbatar da cewa dimokuradiyya ta haifar da ci gaba, da wadata da tsaro ga kowa.















Discussion about this post