Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Pankshin/Kanke/Kanam Yusuf Gagdi, ya rasa tikitin jam’iyyar APC na komawa majalisar tarayya karo na uku.
Gagdi ya sha kaye ne a hannun John Tongshinen a zaɓen fidda gwani na kai tsaye da jam’iyyar ta gudanar a faɗin mazaɓar.
Da yake bayyana sakamakon zaɓen a shalƙwatar mazaɓar da ke Pankshin ranar Lahadi, jami’in gudanar da zaɓen na APC, Monday Daspan, ya ce Tongshinen ya samu ƙuri’u 29,968 yayin da Gagdi ya samu ƙuri’u 5,849.
“Da ikon da aka ba ni a matsayin shugaban wannan kwamiti, ina ayyana Dr John Tongshinen a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na mazabar Pankshin/Kanke/Kanam bisa ga sakamakon da ke gabana,” in ji Daspan.
Yusuf Gagdi a halin yanzu shi ne shugaban kwamitin kula da rundunar sojin ruwa ta majalisar wakilai, yayin da aka gudanar da zaɓen fidda gwanin a ƙananan hukumomi uku da suka haɗa mazabar tarayyar.















Discussion about this post