ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro – Sarkin Fulanin Mubi

by Bello Hamza
6 months ago
Mubi

A ranar Lahadi 30 ga watan Nuwamban 2025 ne mai Martaba Sarkin Mubi ta Jihar Adamawa, Dr. Alhaji Abubakar Isa Ahmadu ya tabbatar wa da Sanata Dr Abdulrahaman Buba Kwacham sarautar Sarkin Fulanin Mubi. Tabbatar da sarautar ya samu sa albarkan Gwamnan Jihar Adamawa Hon. Dr Ahmadu Umaru Fintiri.

Taron tabbatar da sarautar ya gudana ne a unguwar Zone 7 da ke Abuja babbar birnin tarayya Abuja. Inda wasu manyan fadawar masarautar Mubi suka gabatar wa da Sanata Buba Kwacham wasikar nadin.

  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Real Madrid Ta Shiga Halin Damuwa Bayan Wasanni Uku Ba Tare Da Nasara Ba

A cikin jawabinsa bayan miqa masa wasiqar, Sanata Abdulraham Buba Kwacham ya gode wa Sarkin Mubi Dr. Alhaji Abubakar Isa Ahmadu da kuma gwamnan Jihar Adamawa Hon. Dr Ahmadu Umaru Fintiri a kan yadda suka amince da bashi wannan mukamin, ya kuma yi alkawarin gudanar da ayyukan da ke tattare da dukaka darajar masarautar ba tare da nuna bambancin qaliba ko addini ba.

ADVERTISEMENT

 

Ya kuma bayyana cewa, zai yi aiki tukuru domin ganin an samu zaman lafiya a duk inda ake samun matsaloli da Fulani, ya ce, Fulani mutane ne masu son zaman lafiya da kaunar al’umma, a kan haka ya nemi gwamnati ta yi kokarin samar wa al’ummar Fulani ababen more rayuwa a duk inda suke, “Kamar makarantu, asibitoci da magungunan dabbobisu”.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

 

A kan matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan qasar nan, ya ce, al’amari ne da yake bukatar hada hannu ba tare da nuna bambancin kabila ko addini ba, “Lamarin tsaro abu ne da ya shafi kowa da kowa, ya kuma yi alkawarin tabbatar ana yi wa Fulani adalci musamman na ganin an dawo da hanyoyin da shanu ke zirga-zirga (LABI) a shekarun baya, hakan zai rage tashin hankali a tsakanin makiyaya da manoma a qasar nan” in ji shi. Ya kuma yi alkawarin hada hannu da gwamnati don kawo karshen matsalar tsaro a Kawar nan. A jawabinsa na maraba da baki, Hon Ahmad Sajo Geela ya mika godiya ga Masarautar Mubi da gwamnan Jihar Adamawa a kan sarautar da ta ba Sanata Abdulraham Kwacham, ya bayyana cewa, yana da yakinin cewa, Sabon Sarkin Fulanin Mubi zai yi abin da ya kamata musamman ganin cewa, mutum ne mai son mutane kuma kofarsa a buxe take ba tare da nuna banbanci ba. Ya yi addu’ar Allah ya ba shi ikon sauke nauyin da aka dora masa.

Mubi
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 25 A Wani Sabon Hari Kan Iyakar Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 25 A Wani Sabon Hari Kan Iyakar Kano

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.