ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro – Sarkin Fulanin Mubi

by Bello Hamza
7 months ago
Mubi

A ranar Lahadi 30 ga watan Nuwamban 2025 ne mai Martaba Sarkin Mubi ta Jihar Adamawa, Dr. Alhaji Abubakar Isa Ahmadu ya tabbatar wa da Sanata Dr Abdulrahaman Buba Kwacham sarautar Sarkin Fulanin Mubi. Tabbatar da sarautar ya samu sa albarkan Gwamnan Jihar Adamawa Hon. Dr Ahmadu Umaru Fintiri.

Taron tabbatar da sarautar ya gudana ne a unguwar Zone 7 da ke Abuja babbar birnin tarayya Abuja. Inda wasu manyan fadawar masarautar Mubi suka gabatar wa da Sanata Buba Kwacham wasikar nadin.

  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Real Madrid Ta Shiga Halin Damuwa Bayan Wasanni Uku Ba Tare Da Nasara Ba

A cikin jawabinsa bayan miqa masa wasiqar, Sanata Abdulraham Buba Kwacham ya gode wa Sarkin Mubi Dr. Alhaji Abubakar Isa Ahmadu da kuma gwamnan Jihar Adamawa Hon. Dr Ahmadu Umaru Fintiri a kan yadda suka amince da bashi wannan mukamin, ya kuma yi alkawarin gudanar da ayyukan da ke tattare da dukaka darajar masarautar ba tare da nuna bambancin qaliba ko addini ba.

ADVERTISEMENT

 

Ya kuma bayyana cewa, zai yi aiki tukuru domin ganin an samu zaman lafiya a duk inda ake samun matsaloli da Fulani, ya ce, Fulani mutane ne masu son zaman lafiya da kaunar al’umma, a kan haka ya nemi gwamnati ta yi kokarin samar wa al’ummar Fulani ababen more rayuwa a duk inda suke, “Kamar makarantu, asibitoci da magungunan dabbobisu”.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

 

A kan matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan qasar nan, ya ce, al’amari ne da yake bukatar hada hannu ba tare da nuna bambancin kabila ko addini ba, “Lamarin tsaro abu ne da ya shafi kowa da kowa, ya kuma yi alkawarin tabbatar ana yi wa Fulani adalci musamman na ganin an dawo da hanyoyin da shanu ke zirga-zirga (LABI) a shekarun baya, hakan zai rage tashin hankali a tsakanin makiyaya da manoma a qasar nan” in ji shi. Ya kuma yi alkawarin hada hannu da gwamnati don kawo karshen matsalar tsaro a Kawar nan. A jawabinsa na maraba da baki, Hon Ahmad Sajo Geela ya mika godiya ga Masarautar Mubi da gwamnan Jihar Adamawa a kan sarautar da ta ba Sanata Abdulraham Kwacham, ya bayyana cewa, yana da yakinin cewa, Sabon Sarkin Fulanin Mubi zai yi abin da ya kamata musamman ganin cewa, mutum ne mai son mutane kuma kofarsa a buxe take ba tare da nuna banbanci ba. Ya yi addu’ar Allah ya ba shi ikon sauke nauyin da aka dora masa.

Mubi
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 25 A Wani Sabon Hari Kan Iyakar Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 25 A Wani Sabon Hari Kan Iyakar Kano

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.