ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Kalubalanci Duk Wani Yunkuri Na Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya – PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Shugabannin jam’iyyar PDP na kasa sun bayyana damuwarsa kan yiwuwar mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya tilo, inda suka bayyana cewa za su kalubalanci duk wani yunurin jam’iyyar APC mai mulki kan mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya gabanin zaben 2027.

Jam’iyyar PDP ta bayyana hakan ne a lokacin da take jawabi ga shugabannin jam’iyyar na Jihar Akwa Ibom da magoya bayanta da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar yayin ziyarar godiya ga Gwamna Umo Eno ya kai ofishin jam’iyyar.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Shugabar mata ta jam’iyyar PDP ta kasa, Hajiya Amina Darosimi, wacce ta yi magana a madadin kwamitin gudanarwa na kasa, ta lura da irin ci gaban da gwamnatin Gwamna Eno ta samu, inda ta tabbatar da cewa jam’iyyar ta amince da wannan nasarar.

Da take yaba nasarorin da gwamna ya samu a cikin watanni 19 da suka gabata, Darosimi, ta lura da irin kokarin da aka yi wajen gina jihar a karkashinsa. Tana mai bayyana cewa jam’iyyar na alfahari da irin nasarorin da gwamnan ya samu.

Shugabar matar ta ba da tabbacin cewa, “PDP ta ci gaba da jajircewa wajen yin tir da duk wani yunkuri na mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya, domin PDP na bayar da ingantacciyar adawa a cikin al’ummar kasar nan,” kuma ta yi alkawarin goyon bayan jam’iyyar don ganin Gwamna Eno ya samu nasarar lashe wa’adi na biyu. “

Da yake mayar da martani, gwamnan ya nuna jin dadinsa ga jam’iyyar wajen shi ne goyon baya a bangarori daban-daban domin samun nasarar gwamnatinsa tun ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya bayyana cewa ziyarar tasa ta yi daidai da al’adar shugabannin jam’iyyar PDP, inda ya ce jam’iyyar ita ce ta mallaki gwamnatinsa.

Gwamna Eno ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da habaka muradun al’amma domin biyan bukatun jam’iyyar da kuma dorewar farin mutanen Jihar Akwa Ibom.

Gwamna Eno ya ci gaba da bai wa jam’iyyar PDP aminci da suka samu damar yin aiki a gwamnati a bangarori daban-daban da su yi kokarin tabbatar da kyakkyawar alaka da jama’arsu ta yadda za su bunkasa kimarsu ta siyasa a tsakaninsu, wanda hakan zai sa jam’iyyar ta amfana a wajen dorewar shahararta.

Shugaban jam’iyyar PDP a jihar, Elder Aniekan Akpan ya gode wa gwamnan kan ziyarar sabuwar shekara da kuma goyon bayan da yake bai wa jam’iyyar.

Ya kuma mika kudirin jam’iyyar PDP na amincewa da Fasto Eno a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar a zaben 2027 a Jihar Akwa Ibom.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Sin Mai Bude Kofarta Na Maraba Da Cudanyar Al’ummun Duniya

Sin Mai Bude Kofarta Na Maraba Da Cudanyar Al’ummun Duniya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.