ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Kalubalanci Duk Wani Yunkuri Na Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya – PDP

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
PDP

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Shugabannin jam’iyyar PDP na kasa sun bayyana damuwarsa kan yiwuwar mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya tilo, inda suka bayyana cewa za su kalubalanci duk wani yunurin jam’iyyar APC mai mulki kan mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya gabanin zaben 2027.

Jam’iyyar PDP ta bayyana hakan ne a lokacin da take jawabi ga shugabannin jam’iyyar na Jihar Akwa Ibom da magoya bayanta da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar yayin ziyarar godiya ga Gwamna Umo Eno ya kai ofishin jam’iyyar.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Shugabar mata ta jam’iyyar PDP ta kasa, Hajiya Amina Darosimi, wacce ta yi magana a madadin kwamitin gudanarwa na kasa, ta lura da irin ci gaban da gwamnatin Gwamna Eno ta samu, inda ta tabbatar da cewa jam’iyyar ta amince da wannan nasarar.

Da take yaba nasarorin da gwamna ya samu a cikin watanni 19 da suka gabata, Darosimi, ta lura da irin kokarin da aka yi wajen gina jihar a karkashinsa. Tana mai bayyana cewa jam’iyyar na alfahari da irin nasarorin da gwamnan ya samu.

Shugabar matar ta ba da tabbacin cewa, “PDP ta ci gaba da jajircewa wajen yin tir da duk wani yunkuri na mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya, domin PDP na bayar da ingantacciyar adawa a cikin al’ummar kasar nan,” kuma ta yi alkawarin goyon bayan jam’iyyar don ganin Gwamna Eno ya samu nasarar lashe wa’adi na biyu. “

Da yake mayar da martani, gwamnan ya nuna jin dadinsa ga jam’iyyar wajen shi ne goyon baya a bangarori daban-daban domin samun nasarar gwamnatinsa tun ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya bayyana cewa ziyarar tasa ta yi daidai da al’adar shugabannin jam’iyyar PDP, inda ya ce jam’iyyar ita ce ta mallaki gwamnatinsa.

Gwamna Eno ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da habaka muradun al’amma domin biyan bukatun jam’iyyar da kuma dorewar farin mutanen Jihar Akwa Ibom.

Gwamna Eno ya ci gaba da bai wa jam’iyyar PDP aminci da suka samu damar yin aiki a gwamnati a bangarori daban-daban da su yi kokarin tabbatar da kyakkyawar alaka da jama’arsu ta yadda za su bunkasa kimarsu ta siyasa a tsakaninsu, wanda hakan zai sa jam’iyyar ta amfana a wajen dorewar shahararta.

Shugaban jam’iyyar PDP a jihar, Elder Aniekan Akpan ya gode wa gwamnan kan ziyarar sabuwar shekara da kuma goyon bayan da yake bai wa jam’iyyar.

Ya kuma mika kudirin jam’iyyar PDP na amincewa da Fasto Eno a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar a zaben 2027 a Jihar Akwa Ibom.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Sin Mai Bude Kofarta Na Maraba Da Cudanyar Al’ummun Duniya

Sin Mai Bude Kofarta Na Maraba Da Cudanyar Al’ummun Duniya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.