Wani mai neman takarar gwamnan jihar Filato a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, Chief Kefiano Kefas Ropshik, ya bayyana cewa babban burinsa shi ne bai wa al’ummar Filato fifiko a dukkan matakan shugabanci idan aka zaɓe shi.
Ropshik ya ce ya samu nasarar tsallake tantancewar da jam’iyyar ta gudanar domin shiga zaɓen fidda gwani na gwamna mai zuwa a jihar. An gudanar da tantancewar ne a shalƙwatar jam’iyyar PDP da ke Wadata Plaza yayin da jam’iyyar ke ci gaba da shirye-shiryen zaɓen 2027.
Da yake magana bayan tantancewar, ya bayyana matakin a matsayin wani muhimmin ci gaba a burinsa na jagorantar jihar Filato, yana mai bayyana ƙwarin gwuiwa kan manufofinsa da jajircewarsa wajen yi wa jama’a aiki.
“Yau na halarci tantancewa a sakatariyar PDP da ke Wadata Plaza, wani babban mataki a wannan tafiya ta yi wa al’ummar jihar Filato hidima a matsayin gwamna,” in ji shi.
Ya kuma sake jaddada aniyarsa ta gudanar da shugabanci mai fifita jama’a tare da samar da ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar, yana mai amfani da taken “Filato First” domin nuna ƙudurinsa.















Discussion about this post