Kungiyar Manoma ta Kasa (AFAN) ta ce farashin kayan abinci na iya sauka zuwa lokacin girbi mai zuwa idan gwamnatoci suka inganta tsaro tare da rage kudin noma ga manoma.
Mataimakin Shugaban AFAN reshen Jihar Lagos, Mista Shakin Agbayewa, ne ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) ya yi da shi ranar Talata a Lagos.
Agbayewa ya ce kayan abinci na yau da kullum kamar shinkafa, doya, rogo da garin rogo za su fi saukin samu idan manoma suka samu damar noma cikin tsaro tare da samun kayan aikin gona cikin rahusa.
A cewarsa, rashin tsaro, tsadar taki, karin farashin mai da kuma tsadar gudanar da ayyukan gona ne manyan abubuwan da ke haddasa hauhawar farashin abinci a yanzu.
Ya ce: “Dole ne gwamnati ta kasance mai niyya da daukar mataki kai tsaye.
“Farashin kayan noma ya yi tsada. Taki ya yi tsada, yayin da aikin tirekta ya kara tsada saboda hauhawar farashin mai. Duk wadannan abubuwa suna shafar yawan amfanin gona.”
Agbayewa ya ce tsadar noma, sufuri da tsaro daga karshe ana dora su ne kan masu sayen kayan abinci.
Ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai su tallafa wa manoma da kayan noma masu rahusa, inganta hanyoyin karkara, samar da hanyoyin ban ruwa da kuma bashi mai saukin samu.
Ya kuma yi kira da a kara hadin gwiwa da kungiyoyin manoma domin gano hanyoyin magance matsaloli da suka dace da bukatun kowace jiha.
A cewarsa, karin yawan noma a kakar bana zai taimaka wajen rage matsin lamba kan farashin kasuwa.
Agbayewa ya ce Nijeriya na da isasshiyar kasa da ma’aikata da za su iya ciyar da kanta idan aka aiwatar da manufofi masu kyau.
Ya kara da cewa tallafa wa manoma shi ne hanya mafi dorewa wajen rage farashin abinci da tabbatar da daidaiton tattalin arziki.















Discussion about this post