ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Duk Ƴan Dakon Hatsi A Nassarawa Sun Mallaki Katin Zaɓe — Alhaji Danji

by Abubakar Sulaiman
8 months ago

Shugaban Ƙungiyar ƴan Dakon Hatsi ta Jihar Nasarawa, Alhaji Danji Aliyu, ya ce zai gudanar da rangadi a dukkan ƙananan hukumomin jihar domin tabbatar da cewa duk mambobin ƙungiyar sun mallaki katin zaɓe.

Alhaji Danji ya bayyana hakan ne a ofishinsa da ke Lafia, bayan kammala taron addu’ar shiga sabuwar shekarar 2026. Ya jaddada cewa katin zaɓe hakki ne na kowane ɗan ƙasa, wanda ke ba shi damar zaɓar shugabannin da yake ganin za su yi masa adalci.

  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa
  • Jam’iyyar NNPP Ta Yi Watsi Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Dungurawa A Kano

Ya ce ƙungiyar ƴan dakon hatsi na da mambobi masu yawa a faɗin jihar, kuma an ƙuduri aniyar tabbatar da cewa kowane mamba, tare da iyalansa, sun mallaki katin zaɓe domin shirye-shiryen zaɓe na gaba. Ya kuma gode wa mambobi da tsofaffin shugabannin ƙungiyar bisa amincewar da suka sake ba shi na jagorantar ƙungiyar na tsawon ƙarin shekaru uku.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Shugaban ƙungiyar ƴan dakon hatsi ta ƙasa, Alhaji Hamza Abdullahi, ya shawarci mambobin da su rungumi yin tattali don gaba. Ya ce duk abin da mutum ya samu daga aikin dakon hatsi, ya ware wani kaso domin ajiya, yana mai jaddada cewa hakan zai taimaka musu su fara kasuwanci a nan gaba, musamman ganin cewa aikin na buƙatar ƙarfi wanda kan ragu da lokaci.

An gudanar da taron addu’ar ne a ranar 1 ga Janairu, 2026, a zauren ofishin ƙungiyar da ke kasuwar kayan hatsi ta Kwandare a Lafia, inda malamai da dama suka yi addu’o’i ga ƙungiyar, da shugabanninta, da Jihar Nasarawa da ƙasa baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11

MASU ALAKA

Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Next Post
Komawar Abba APC: Maslahar Al’umma Ko Kasuwar Bukata?

Komawar Abba APC: Maslahar Al'umma Ko Kasuwar Bukata?

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.