ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Aringizon Kasafin 2024: Majalisa Ta Jingine Sanata Ningi Bayan Ya Farke Laya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Sanata

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Majalisar dattawan Nijeriya ta dakatar da shugaban kungiyar sanatocin arewa, Abdul Ningi na tsawon watanni uku bisa zargin an cusa Naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Shugaban majalisar dattawan, Sanata Godswill Akpabio ne ya sanar da daukan wannan mataki a zaman majalisar da ya gudana bayan sauraron korafin da aka shigar a kansa.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Mamba a kwamitin kasain kudi na majaliar dattawa, Sanata Jimoh Ibrahim, mai wakiltar Ondo ta kutu, shi ne ya fara gabatar da kudurin dakatar da Sanata Ningi na tsawon wata 12, bisa zarginsa da ba da bayanai karya wanda suke daidai da aikata babban laifi, da kuma hargitsa zaman lafiya a zauren majalisar dokokin kasa.

Sanata Ede Daminone, mai wakiltar Delta ta tsakiya, ya bayyana cewa tun dai an bai wa Sanata Ningi damar bayar da hakuri kuma ya ki, to shi ya goyi bayan kurin dakatar da shi na tsawon watanni 12.

Amma Sanata Asukuo Ekpenyong, mai wakiltar Kuros Riba ta kudu ya bukaci a dakatar da Sanata Ningi na tsawon wata 6, yayin da Sanata Buhari Abdulfatai ya amince a dakatar da shi na tsawon wata 3.

Sanata Garba Musa Maidoki, mai wakiltar Kebbi ta kudu ya amince da dakatar da Ningi har tsawon wata 3 tun da dai ya bayyana kalaman da ba daidai ba kuma ya ki bayar da hakuri.

A nasa bangaren, Sanata Sani Musa, mai wakiltar Neja ta gabas, ya ce a takatar da Sanata Ningi na tsawon watanni uku tare da ba shi damar rubuta wasikar bayar da hakuri.

Bayan jin ra’ayoyin ‘yan majalisar, daga karshe dai shugaban majalisar dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya takatar da Sanata Ningi daga majalisa na tsawon wata 3.

Nan take Sanata Ningi ya bar zauren majalisar dattawan tare da daukar takardunsa a hannu, yayin da wani dogarin majalisan yana yi masa rakiya har zuwa waje.

Wannan lamari ya janyo cece-ku-ce a zauren majalisa a ranar Talata da ta gabata, wanda ake ganin cewa Sanata Ningi ya fare laya, yayin da ita kuma majalisa ta sagale shi na wata 3.

Shugaban majalisan ya yanke wannan hukunci ne bisa dogaro da sashi na 66 (1) da kuma sahi na 2, wadanda suka bai wa shugaban majalisa karfin ikon ladaftar da duk wani ‘yan majalisa da ya yi laifi tare da bai wa dokarin majalisa damar fitar da shi waje.

Kazalika, Sanata Ningi ya sauka daga mukaminsa na shugaban kungiyar sanatocin arewa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sanata Ningi, wanda shi ne shugaban kwamitin kidaya na majalisar dattaea, ya bayyana murabus dinsa daga shugabancin kungiyar sanatocin arewa.

A cikin wasikar da aka bai wa sakataren kungiyar sanatocin arewa mai taken yin murabus, Sanata Ningi ya ce yin murabus dinsa ya sama wajibi bisa abubuwa da suke faruwa a halin yanzu.

“Ina mai mika godiyata ta musamman ga kungiyar sanatocin arewa da suka ba ni dama na shugabanci na tsawon wata 8, a wannan muhimmin kungiya. Ina da yakinin cewa wannan kungiya tana da matukar muhimmanci wajen kawo abubuwan da za su bunkasa yankin arewacin Nijeriya,” in ji Ningi.

Jerin Sanatocin Da Aka Dakatar Tun Daga 1999

An dakatar da sanatan Ogun ta tsakiya, Femi Okurounmu a 1999.

Laifinsa: An zarge shi da tunzura sanatoci wajen shirin tsige Obasanjo.

Haka kuma an dakatar da sanata mai wakiltar Benuwai ta arewa, Joseph Waku, a watan Fabrairun 2000.

Laifin da ya aikata: Yana kira da a yi juyin mulki bayan komawa mulkin dimokuradiyya da wata 8.

An dakatar da sanatan Imo ta yamma, Arthur Nzeribe a watan Oktoban 2002.

Laifinsa: Yin wasu ayyuka da ba su dace ba a majalisa.

Sannan an dakatar da sanatan Neja ta tsakiya, Isah Mohammed a watan Oktoban 2004.

Laifinsa: Marin Sanata Iyabo Anisulowo.

An dakatar da sanatan Borno ta kudu, Ali Ndume a 2017.

Laifinsa: Shigo da motocin kirar Range Robe da takardun bogi bisa sa sunan Bukola Saraki kuma na Dino Melaye ne.

An dakatar da sanatan Delta ta tsakiya, Obie Omo-Agege a 2018, bisa jagorantar wata tawaga da take a dawa da shugaban majalisar dattawa.

Haka kuma an dakatar da sanatan Bauch ta tsakiya, Abdul Ningi. An dakatar da shi ne a 2024 bisa bayar da bayanan karya kan aringizon kasafin kudin 2024 na naira tiriliyan 3.7.

Sanata
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Hisbah Ta Kama Motoci 3 Makare Da Giya A Kano

Hisbah Ta Damke Mutum 14 Bisa Zargin Fasikanci Lokacin Ramadan A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.