ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Aringizon Kasafin 2024: Majalisa Ta Jingine Sanata Ningi Bayan Ya Farke Laya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Sanata

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Majalisar dattawan Nijeriya ta dakatar da shugaban kungiyar sanatocin arewa, Abdul Ningi na tsawon watanni uku bisa zargin an cusa Naira tiriliyan 3.7 a cikin kasafin kudin 2024.

Shugaban majalisar dattawan, Sanata Godswill Akpabio ne ya sanar da daukan wannan mataki a zaman majalisar da ya gudana bayan sauraron korafin da aka shigar a kansa.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Mamba a kwamitin kasain kudi na majaliar dattawa, Sanata Jimoh Ibrahim, mai wakiltar Ondo ta kutu, shi ne ya fara gabatar da kudurin dakatar da Sanata Ningi na tsawon wata 12, bisa zarginsa da ba da bayanai karya wanda suke daidai da aikata babban laifi, da kuma hargitsa zaman lafiya a zauren majalisar dokokin kasa.

Sanata Ede Daminone, mai wakiltar Delta ta tsakiya, ya bayyana cewa tun dai an bai wa Sanata Ningi damar bayar da hakuri kuma ya ki, to shi ya goyi bayan kurin dakatar da shi na tsawon watanni 12.

Amma Sanata Asukuo Ekpenyong, mai wakiltar Kuros Riba ta kudu ya bukaci a dakatar da Sanata Ningi na tsawon wata 6, yayin da Sanata Buhari Abdulfatai ya amince a dakatar da shi na tsawon wata 3.

Sanata Garba Musa Maidoki, mai wakiltar Kebbi ta kudu ya amince da dakatar da Ningi har tsawon wata 3 tun da dai ya bayyana kalaman da ba daidai ba kuma ya ki bayar da hakuri.

A nasa bangaren, Sanata Sani Musa, mai wakiltar Neja ta gabas, ya ce a takatar da Sanata Ningi na tsawon watanni uku tare da ba shi damar rubuta wasikar bayar da hakuri.

Bayan jin ra’ayoyin ‘yan majalisar, daga karshe dai shugaban majalisar dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya takatar da Sanata Ningi daga majalisa na tsawon wata 3.

Nan take Sanata Ningi ya bar zauren majalisar dattawan tare da daukar takardunsa a hannu, yayin da wani dogarin majalisan yana yi masa rakiya har zuwa waje.

Wannan lamari ya janyo cece-ku-ce a zauren majalisa a ranar Talata da ta gabata, wanda ake ganin cewa Sanata Ningi ya fare laya, yayin da ita kuma majalisa ta sagale shi na wata 3.

Shugaban majalisan ya yanke wannan hukunci ne bisa dogaro da sashi na 66 (1) da kuma sahi na 2, wadanda suka bai wa shugaban majalisa karfin ikon ladaftar da duk wani ‘yan majalisa da ya yi laifi tare da bai wa dokarin majalisa damar fitar da shi waje.

Kazalika, Sanata Ningi ya sauka daga mukaminsa na shugaban kungiyar sanatocin arewa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sanata Ningi, wanda shi ne shugaban kwamitin kidaya na majalisar dattaea, ya bayyana murabus dinsa daga shugabancin kungiyar sanatocin arewa.

A cikin wasikar da aka bai wa sakataren kungiyar sanatocin arewa mai taken yin murabus, Sanata Ningi ya ce yin murabus dinsa ya sama wajibi bisa abubuwa da suke faruwa a halin yanzu.

“Ina mai mika godiyata ta musamman ga kungiyar sanatocin arewa da suka ba ni dama na shugabanci na tsawon wata 8, a wannan muhimmin kungiya. Ina da yakinin cewa wannan kungiya tana da matukar muhimmanci wajen kawo abubuwan da za su bunkasa yankin arewacin Nijeriya,” in ji Ningi.

Jerin Sanatocin Da Aka Dakatar Tun Daga 1999

An dakatar da sanatan Ogun ta tsakiya, Femi Okurounmu a 1999.

Laifinsa: An zarge shi da tunzura sanatoci wajen shirin tsige Obasanjo.

Haka kuma an dakatar da sanata mai wakiltar Benuwai ta arewa, Joseph Waku, a watan Fabrairun 2000.

Laifin da ya aikata: Yana kira da a yi juyin mulki bayan komawa mulkin dimokuradiyya da wata 8.

An dakatar da sanatan Imo ta yamma, Arthur Nzeribe a watan Oktoban 2002.

Laifinsa: Yin wasu ayyuka da ba su dace ba a majalisa.

Sannan an dakatar da sanatan Neja ta tsakiya, Isah Mohammed a watan Oktoban 2004.

Laifinsa: Marin Sanata Iyabo Anisulowo.

An dakatar da sanatan Borno ta kudu, Ali Ndume a 2017.

Laifinsa: Shigo da motocin kirar Range Robe da takardun bogi bisa sa sunan Bukola Saraki kuma na Dino Melaye ne.

An dakatar da sanatan Delta ta tsakiya, Obie Omo-Agege a 2018, bisa jagorantar wata tawaga da take a dawa da shugaban majalisar dattawa.

Haka kuma an dakatar da sanatan Bauch ta tsakiya, Abdul Ningi. An dakatar da shi ne a 2024 bisa bayar da bayanan karya kan aringizon kasafin kudin 2024 na naira tiriliyan 3.7.

Sanata
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Hisbah Ta Kama Motoci 3 Makare Da Giya A Kano

Hisbah Ta Damke Mutum 14 Bisa Zargin Fasikanci Lokacin Ramadan A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.