ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙarin Albashin Sojoji Ya Tunzura Ƙungiyar Ƙwadago Neman Ƙari

by Sani Anwar
3 weeks ago

Sabon tsarin albashin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi kwanan nan ga ma’aikatan rundunar soji, zai ɗaga albashin Janar na soja zuwa naira miliyan 3.25, yayin da na ƙananan sojoji zai koma naira 187,200.

Wannan ƙarin albashi, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Satumbar 2026, ya ƙunshi ƙarin da ya kama daga kashi 30 zuwa kashi 80 ga matsayi na soja daban-daban.

Ana sa ran sojoji kimanin 250,000 ne za su ci gajiyar wannan sabon tsarin albashi, wanda zai ƙara yawan kuɗin da ake kashewa, wajen biyan albashin sojojin a shekara daga naira biliyan 660 zuwa naira biliyan 924, kamar yadda wata sanarwa daga mai bai wa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ta bayyana.

ADVERTISEMENT

A ƙarƙashin sabon tsarin, jami’ai masu matsayi sama da na Kanal, za su samu ƙarin albashi na kashi 30. Wannan ya shafi Birgediya-janar, Manjo-janar, Laftanar-janar da kuma Janar.

Ma’aikata daga matsayin Kanal zuwa Waran ofisa, za su samu ƙarin kashi 50, yayin da waɗanda ke matsayin ‘Priɓate’ zuwa Sagen za su samu ƙarin kashi 80.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ministan tsaro, Christopher Musa ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi da tashar ‘News Central’ a watan da ya gabata cewa, gwamnatin Tinubu ta ƙara mafi ƙarancin albashin sojoji daga naira 49,000 zuwa naira 100,000.

Wani nazari da jaridar Daily Trust ta gudanar ya nuna cewa, naira 100,000 ɗin za ta iya ciyar da soja na tsawon kwana 21 ne kawai, bisa la’akari da rahoton Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), kan kuɗin abinci mai gina jiki (CoHD), wanda ya sanya kuɗin abinci mai gina jikin ko karin kumallo, ko abincin rana ko na dare ga mutum ɗaya a kan naira 1,589 a kowace rana.

Nazarin ya kuma nuna cewa, sojoji a wasu ƙasashen na Afirka, kamar Afirka ta Kudu, Nijar da Jamhuriyar Benin, suna samun albashin da ya zarce na takwarorinsu na Nijeriya da kashi 200 zuwa kashi 800.

Ƙungiyoyin farar hula, sun yi tambaya kan ko wannan albashin zai isa ya kula da soja da iyalinsa a cikin yanayin tattalin arziƙin da ake ciki a halin yanzu, inda farashin kayan masarufi ke ci gaba da hauhawa. Haka kuma, tsohon kakakin rundunar soji, Manjo Janar John Enenche (mai ritaya), ya yi kira da a ƙara albashin sojojin, inda ya ba da shawarar a sanya mafi ƙarancin albashin wata ya zama daga naira 250,000; hakan ya biyo bayan ganin cewa, albashin da ake biya a yanzu bai dace da yanayin tattalin arziƙin ƙasar ko kuma irin sadaukarwar da aikin soja ke buƙata ba.

Da yake yin tsokaci a kan batun ƙarin albashin, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa; matakin ƙara albashin sojojin na nufin karrama sadaukarwar da maza da matan rundunar ke yi, wajen tunkarar ƴan fashi, masu garkuwa da mutane, da ƴan ta’adda.

“Dole ne mu tallafa wa maza da matan da ke tabbatar da tsaronmu a gidajenmu tare da nuna godiya a kan ayyukan da suke yi wa ƙasarmu,” in ji Tinubu a cikin sanarwar.

Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin sojoji tare da inganta rundunar sojin ƙasa ta hanyar samar da sabbin makamai da kayan aikin zamani na fasaha.

Sojoji
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sojoji

Gwamnati Za Ta Ɗauki Ƴan Sintiri Aikin Kare Hanyar Abuja Zuwa Kaduna Daga Ɓata-gari — Umahi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.