ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙaruwar Hare-haren ‘Yan Bindiga: Gwamnan Zamfara Ya Gana Da Shugaban Ƙasa

by Leadership Hausa
2 years ago
yan bindiga

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya gana da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu domin tattaunawa kan yadda ake samun ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga da matsalolin tsaro a jihar.

An yi ganawar ce a ranar Talata cikin sirri a ofishin shugaban ƙasa da ke fadar Aso Rock Villa, Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa Gwamnan ya yi wa Shugaba Tinubu bayani kan ƙaruwar matsalar tsaro a Zamfara, musamman yadda ake ci gaba da kai hare-hare a wasu yankuna.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, shugaba Tinubu da Gwamnan sun tattauna dabaru da matakai daban-daban na shawo kan matsalar tsaro da suka haɗa da ƙara yawan jami’an tsaro, tattara bayanan sirri da kuma shirye-shiryen haɗa kai da al’umma.

  • Abin da muka tattauna da Shugaba Tinubu kan sha’anin tsaron Zamfara – Gwamnan Jihar Zamfara
    https://youtu.be/F-sMeKX9VM4

Ganawar ya kuma bayyana buƙatar magance matsalolin da suka addabi jihar, kamar talauci da rashin aikin yi, waɗanda suke zama silar yawaitar aikata miyagun laifuka a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Wani ɓangare na sanarwar ta ce: “A yau ne Gwamna Dauda Lawal ya gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa, inda suka tattauna muhimman batutuwan da suka shafi matsalar tsaro a Jihar Zamfara”.

“A yayin ganawar sirrin, Gwamna Lawal ya sanar da shugaban ƙasa cewa, a cikin shekaru 13 da suka gabata, jihar Zamfara ta zama cibiyar ’yan bindiga a Arewa maso Yammacin Nijeriya.”

“Gwamnan ya roƙi shugaba Tinubu da ya shiga tsakani wajen kawo isassun sojoji, makamai, da kuma kayan aiki, domin ba su isa ba a Zamfara. Ya kuma buƙaci isassun tallafi ta sama don taimaka wa sojojin ƙasa,” in ji sanarwar.

Ta ce, “Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa gwamnan tabbacin ba da duk wani muhimmin tallafi da dabaru ga jami’an tsaro domin tabbatar da maido da zaman lafiya a Zamfara.”

Sanarwar ta ce, “Bugu da ƙari, shugaban ƙasar ya sake jaddada matsayin gwamnatin sa na ƙin yin sulhu da ’yan bindiga da kuma biyan kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane, matakin da ya yi imanin zai ƙara musu ƙwarin gwiwa ne kawai.”

  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga
yan bindiga
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
boao

Ana Sa Ran Dandalin Boao Na Bana Zai Hallara Mutane Kimanin 2,000

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.