ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙasashen Afirka 10 Da Suka Fi Sayen Makaman Yaƙi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 weeks ago
10

Duk da cewa sayen makamai da ƙasashen Afirka ke yi daga ƙasashen ƙetare ya ragu da kimanin kashi -41, kamar yadda Cibiyar Bincike kan Zaman Lafiya ta Stockholm (SIPRI) ya nuna, amma ƙasashen Afirka da ke kudu da hamadar Sahara sun ƙara yawan makaman da suke saye.

Wannan labarin ya yi nazari kan ƙasashen Afirka 10 da ke kudu da hamadar Sahara waɗanda suka fi sayen makamai, kamar yadda cibiyar ta SIPRI ta bayyana.

Ƙasashe kamar Nijeriya  da Senegal da Mali na daga cikin waɗanda suka fi sayen makamai daga ƙasashen ƙetare, in ji rahoton, kamar yadda darakatan nazari kan harkar makamai na cibiyar, Dr Mathew George ya yi bayani.

ADVERTISEMENT

Nijeriya

Nijeriya ce ƙasar da ta fi kowace sayen makamai daga ƙetare a cikin ƙasashen Afirka da ke kudu da hamada.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Nijeriya ce ke da kashi 16 na yawan makaman da ƙasashen ke saye.

Makaman da Nijeriya ta fi saye su ne jiragen yaƙi da jiragen soji masu saukar ungulu da motocin sulke da jiragen ruwa da kuma jirage marasa matuƙa.

Nijeriya na sayen makamanta ne daga ƙasashe daban-daban. Daga cikin irin waɗannan ƙasashe akwai Turkiyya da Koriya ta Kudu da China da Netherlands da Faransa da Italiya da Brazil da Amurka da Rasha da Afirka ta Kudu da Pakistan da Canada da Saudiyya da Austria da kuma Malaysia.

Nijeriya ce ke sayen kashi ɗaya cikin shida na makaman da ke zuwa ƙasashen Afirka da ke kudu da Sahara.

Senegal

Senegal ta yi yunƙuri sosai wajen haɓaka ƙarfin sojinta. An yi ƙiyasin cewa tana da kashi 8.8 na makaman da ƙasashen Afirka ke saye.

Ita ce ƙasa ta biyu mafi sayen makamai a yankin, inda take sayen jiragen sojin ruwa domin tsaron bakin gaɓar tekunta da haƙar ɗanyen man fetur a teku, sannan kuma tana sayen jiragen yaƙi da kuma na tattara bayanan sirri.

Senegal ta sayi makaman kai hari kan jiragen ruwa da motoci masu sulke da makaman atilare.

Ƙasar na sayen makamai ne daga ƙasashen Faransa da Bulgaria da China da Afirka ta Kudu da Indonesia da Denmark da Italiya da Jamus da Amurka da Turkiyya da Spaniya da kuma Canada.

Mali

Ƙarfin sojin ƙasar Mali ya riƙa ƙatuwa tun daga shekara ta 2020. Yaƙin da ƙasar ke yi da ƙungiyoyin ƴan bindiga shi ne silar ƙara ƙarfin sojin.

Mali ta zamo ƙasa ta uku mafi sayen makamai tsakanin ƙasashen Afirka, kuda da Sahara.

Ƙasar ta zuba maƙudan kuɗaɗe, wanda hakan ya sanya take da kashi 80 na dukkanin makaman da ƙasashen Afirka, kudu da Sahara ke saye.

Mali ta sauya ƙasashen da take hulɗar tsaro da su, inda yanzu ta karkata zuwa ga Rasha bayan saɓanin da ta samu da Faransa.

Mali ta sayi kayan yaƙi kamar motpoci masu sulke da jiragen ɗaukar dakaru da jiragen yaƙi da manyan makaman atilare da makamai masu linzami da sauran su.

Ethiopia

Sanadiyyar rikicin gida na yankin Tigray, ƙasar Habasha ta riƙa sayen jirage marasa matuƙa, waɗanda ta dogara sosai a kansu.

Haka nan ƙasar ta sayi jiragen saman yaƙi da makaman atilare da motocin sulke da na ɗaukar dakaru sai kuma jiragen horo da na kai hari.

Ethiopia na sayen makamanta ne daga ƙasashen Rasha da Turkiyya da Iran da Amurka da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da kuma Bosnia.

Angola

Angola wadda ta daɗe tana fama da yaƙi ta shafe kimanin shekara biyar tana sayen makamai, inda makaman da ta saya suka kai kashi 4.7 na makaman da ke shiga ƙasashen Afirka, kuda da Sahara.

Angola ta fi mayar da hankali ne kan tsaron bakin iyaka da kuma sararin samaniyarta.

Makaman da take saye sun hada da injunan jiragen sama da jiragen kwale-kwalen soji.

Ƙasar kan sayi makamanta ne daga ƙasashe kamar Spanin da Belarus da Faransa da kuma Canada.

Kenya

Kenya na fuskantar matsalar tsaro musamman a kan iyakokinta, inda ake sake samun ɓarkewar hare-haren ƙungiyar Al-Shabab da kuma sauran ayyukan laifuka, musamman a arewa maso gabashin ƙasar da kuma Nairobi, babban birnin ƙasar.

Domin shawo kan matsalar, Kenya ta kashe maƙudan kuɗaɗe wajen sayen makamai.

Ta sayi makamai kamar jiragen ɗaukar dakaru da jiragen saman yaƙi da makamai masu linzami masu cin dogon zango da jirage marasa matuƙa na Bayraktar TB-2 da kuma jirage masu saukar ungulu daban-daban, ciki har da Hughes-500D.

Ƙasar na sayen makamai ne daga ƙasashe kamar Hadaddiyar Daular Larabawa da Jamus da Isra’ila da Turkiyya da Amurka da kuma Koriya ta Arewa.

Mauritania

Duk da cewa Mauritania na daga cikin ƙasashe masu zaman lafiya a yankin Sahel, ƙasar na fuskantar barazanar hare-haren ta’addanci a kan iyakokinta na arewa da kuma gabashi, musamman yankunan da take iyaka da ƙasashen Algeria da Mali.

Ƙasar ta sayi makamai masu linzami da ke kai hari kan tankokin yaƙi da jiragen jigilar dakaru da sauran motocin yaƙi, sannan ta sayi garkuwa daga makamai da kuma motocin sulke.

Burkina Faso

Burkina Faso ta shafe shekaru tana fama da rikicin ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi, lamarin da ya haifar da ɗimbin asarar rayuka da tarwatsa al’umma daga muhallansu.

Ƙasar ta sayi makamai masu linzami da bama-bamai da motocin sulke da jiragen yaƙi da masu saukar ungulu da makaman atilare da kuma jirage marasa matuƙa da sauran su.

Iɓory Coast

Duk da cewa akwai kwanciyar hankali a kudancin ƙasar, Cote d’Iɓoire na sanya ido sosai kan yankunan arewaci, inda take iyaka da Burkina Faso da kuma Mali, wuraren da ake samun barazanar hare-haren masu iƙirarin jihadi.

Iɓory Coast ta sayi makamai da suka haɗa da jirage masu saukar ungulu na AS-350 da H-125, da jirage masu saukar ungulu na kai hari da motocin sulke da kuma ƙananan jiragen ruwan sintiri na gaɓar teku.

Rwanda

Rwanda ta ƙara ƙarfin garkuwarta ta hare-garen sama, inda makaman da ta saya suka kai kashi 3.5 na makaman da ƙasashen Afirka, kudu da Sahara ke shigarwa.

Makaman da Rwanda ta saya sun haɗa da jirage masu saukar ungulu na kai hare-hare da motocin sulke da makaman kakkaɓo makamai masu linzami da kuma wasu da dama.

Me Ya Sa Trump Ke Neman Ɗauki Daga Ƙungiyar NATO A Yaƙin Iran?

Shugaba Trump ya ce yana tattaunawa da ƙasashe da dama domin taimakawa wajen ƙwace ikon mashigar Hormuz a daidai lokacin da yaƙinsa da Iran ke ci gaba da illa ga tattalin arzikin duniya.

Sai dai Mista Trump ya yi gargaɗi ga ƙungiyar tsaro ta NATO idan har ba ta taimaki Amurka ba.

“NATO za ta fuskanci mummunar makoma,” kamar yadda shugaban ya bayyana a wata hira da ya yi da jaridar Financial Times.

Shugaban ya sake yin kira ga ƙasashe su shiga ƙoƙarin tabbatar da buɗe mashigar Hormuz da yake yi domin ba jiragen ruwa damar tsallake shingen Iran.

Ya ce Amurka ta taimaka wa Ukraine a yaƙinta da Rasha, don haka yana tsammanin taimakon ƙasashen Turai kan babbar hanyar ruwa ta Hormuz da Iran ta toshe.

Rufe mashigar dai ya haifar tsadar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya.

Mista Trump ya kuma ce zai jinkirta taron da zai yi da shugaban China Ɗi Jinping yayin da yake matsin lamba ga taimakon China domin buɗe mashigar.

Trump ya ce China da ƙasashen Turai da dama sun fi dogaro fiye da Amurka kan man da ke fitowa daga yankin Tekun Fasha.

“Waɗanda suka fi amfana da mashigin ne ya kamata su taimaka domin tabbatar da wani mugun abu bai faru ba a can,” in ji Trump.

Ya shaida wa manema labarai cewa Amurka na tattaunawa da kusan ƙasashe bakwai domin neman taimakon su sa hannu wajen ceto mashigar Hormuz.

Tuni ƙasashen Japan da Australia suka ce ba za su tura sojojin ruwa ba. Amma Japan ta ce za ta fara fitar da rarar manta domin rage giɓin da na Iran ya haifar, duk da cewa ita ma ta dogara ne da man da ke fitowa daga yankin Gabas Ta Tsakiya.

Babu tabbas game da tsawon lokacin da yaƙin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran zai ɗauka da kuma tasirin da zai yi ga kasuwar mai a duniya, inda farashin ɗanyen mai ya yi tashin gwauron zaɓi a cikin makwanni biyun da suka gabata sakamakon ƙarancinsa.

10
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Kayayyakin Afrika Da Dama Sun Samu Sahalewar Kwastam A Tashoshin Ruwa Na Sin Tun Bayan Kaddamar Da Manufar Soke Haraji

Kayayyakin Afrika Da Dama Sun Samu Sahalewar Kwastam A Tashoshin Ruwa Na Sin Tun Bayan Kaddamar Da Manufar Soke Haraji

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.