ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar NUJ Ta Karrama Shugaba Da Babban Editan Kamfanin LEADERSHIP A Abuja

by Sani Anwar
4 months ago

A ranar Talata ne Shugabar kamfanin jaridar LEADERSHIP Zainab Nda-Isaiah da Babban Editan Jaridar Mista Azu Ishiekwene suka karɓi lambar girmamawa daga ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa reshen Babban Birnin Taratyya Abuja.

A jawabin ta, Shugabar Jaridar LEADERSHIP, Zainab Nda-Isaiah, ta yaba da tsayin daka, jajircewa da kuma ƙwarewar ƴan jaridan Nijeriya, inda ta bayyana jajircewarsu a matsayin wani ginshiƙi na ɗorewar demokuraɗiyya, duk da cewa; suna gudanar da aikin nasu cikin yanayi mai matuƙar wahala.

Ta gabatar da wannan yabo ne a ranar Talata a Abuja, yayin bikin makon manema labarai na ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa (NUJ), na 2026.

ADVERTISEMENT

Da take magana a wajen taron ƙwararrun, Nda-Isaiah ta bayyana yadda ta samu kanta a shugabancin jaridar LEADERSHIP, inda ta bayyana cewa; ta ɗauki gagarumin nauyi tun a farko, wanda ba ta taɓa tsammanin ɗauka ba.

Ta ce: “Tafiya ce wadda kawai ta zo min ɓagatatan, wadda kuma dole ne na sanya takalmin, wanda ko da wasa ban taɓa tsammanin zan iya sanyawa ba,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Kazalika, ta danganta ci gaban kafafen yaɗa labaru da jajircewar ƴan jarida da kuma ƙwararrun, waɗanda a cewarta; suke jajircewa wajen ganin cewa, “duk abin da Nijeriya ta samar, za mu faɗa, ta hanyar jin muryoyinmu.”

Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida, a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin siyasa daban-daban.

Haka zalika, ta yaba wa ƴan jaridar, sakamakon kiyaye mutuncin sana’ar da kuma ci gaba da faɗin gaskiya ga masu mulki, duk kuwa da kasadar da ke tattare da yin hakan.

Ta kuma ƙara da cewa, ƴan jarida sukan yi aiki a wurare masu matuƙar haɗari, musamman ta fuskar faɗin gaskiya, amma duk da haka suna ci gaba da kiyaye ƙa’idojin  da kuma yin kula a cikin rahotannin da suke bayarwa.

Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin ƴan siyasa daban-daban.

Shugabar Jaridar LEADERSHIP ɗin, ta kuma yaba wa manyan ƴan jarida, ciki har da Babban Editan Jaridar, Mista Azu, wanda ta bayyana a matsayin ginshiƙin bayar da tallafi, wanda jajircewarsa take taimaka wa ƙungiyar.

“Ba zan iya bayyana irin tallafi da gudunmawar da shi kansa da sauran mutanen da ke wannan kamfani na LEADERSHIP suka bayar ba, shi ya sa har yanzu muke tsaye da ƙafafunmu,” in ji ta.

Nda-Isaiah, wacce ta yarda da cewa; ita ba ƙwararriyar ƴar jarida ba ce, amma kuma ta dangantakar danginta da wannan aiki na jarida, inda ta bayyana shi a matsayin sana’a mai tushe da sha’awa da kuma gado.

A ƙarshe, ta bayyana godiyarta ga ƴan jarida, kan ci gaba da yi wa ƙasa hidima, inda ta ce; tsayin daka da sadaukarwar da suke bayarwa ta sa sana’ar take ci gaba da wanzuwa tsawon zamani.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Sanata Jibrin Ya Musanta Janyewa Daga Takarar Sanatan Kogi Ta Gabas

Sanata Jibrin Ya Musanta Janyewa Daga Takarar Sanatan Kogi Ta Gabas

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.