ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar NUJ Ta Karrama Shugaba Da Babban Editan Kamfanin LEADERSHIP A Abuja

by Sani Anwar
1 month ago

A ranar Talata ne Shugabar kamfanin jaridar LEADERSHIP Zainab Nda-Isaiah da Babban Editan Jaridar Mista Azu Ishiekwene suka karɓi lambar girmamawa daga ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa reshen Babban Birnin Taratyya Abuja.

A jawabin ta, Shugabar Jaridar LEADERSHIP, Zainab Nda-Isaiah, ta yaba da tsayin daka, jajircewa da kuma ƙwarewar ƴan jaridan Nijeriya, inda ta bayyana jajircewarsu a matsayin wani ginshiƙi na ɗorewar demokuraɗiyya, duk da cewa; suna gudanar da aikin nasu cikin yanayi mai matuƙar wahala.

Ta gabatar da wannan yabo ne a ranar Talata a Abuja, yayin bikin makon manema labarai na ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa (NUJ), na 2026.

ADVERTISEMENT

Da take magana a wajen taron ƙwararrun, Nda-Isaiah ta bayyana yadda ta samu kanta a shugabancin jaridar LEADERSHIP, inda ta bayyana cewa; ta ɗauki gagarumin nauyi tun a farko, wanda ba ta taɓa tsammanin ɗauka ba.

Ta ce: “Tafiya ce wadda kawai ta zo min ɓagatatan, wadda kuma dole ne na sanya takalmin, wanda ko da wasa ban taɓa tsammanin zan iya sanyawa ba,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Kazalika, ta danganta ci gaban kafafen yaɗa labaru da jajircewar ƴan jarida da kuma ƙwararrun, waɗanda a cewarta; suke jajircewa wajen ganin cewa, “duk abin da Nijeriya ta samar, za mu faɗa, ta hanyar jin muryoyinmu.”

Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida, a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin siyasa daban-daban.

Haka zalika, ta yaba wa ƴan jaridar, sakamakon kiyaye mutuncin sana’ar da kuma ci gaba da faɗin gaskiya ga masu mulki, duk kuwa da kasadar da ke tattare da yin hakan.

Ta kuma ƙara da cewa, ƴan jarida sukan yi aiki a wurare masu matuƙar haɗari, musamman ta fuskar faɗin gaskiya, amma duk da haka suna ci gaba da kiyaye ƙa’idojin  da kuma yin kula a cikin rahotannin da suke bayarwa.

Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin ƴan siyasa daban-daban.

Shugabar Jaridar LEADERSHIP ɗin, ta kuma yaba wa manyan ƴan jarida, ciki har da Babban Editan Jaridar, Mista Azu, wanda ta bayyana a matsayin ginshiƙin bayar da tallafi, wanda jajircewarsa take taimaka wa ƙungiyar.

“Ba zan iya bayyana irin tallafi da gudunmawar da shi kansa da sauran mutanen da ke wannan kamfani na LEADERSHIP suka bayar ba, shi ya sa har yanzu muke tsaye da ƙafafunmu,” in ji ta.

Nda-Isaiah, wacce ta yarda da cewa; ita ba ƙwararriyar ƴar jarida ba ce, amma kuma ta dangantakar danginta da wannan aiki na jarida, inda ta bayyana shi a matsayin sana’a mai tushe da sha’awa da kuma gado.

A ƙarshe, ta bayyana godiyarta ga ƴan jarida, kan ci gaba da yi wa ƙasa hidima, inda ta ce; tsayin daka da sadaukarwar da suke bayarwa ta sa sana’ar take ci gaba da wanzuwa tsawon zamani.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Sanata Jibrin Ya Musanta Janyewa Daga Takarar Sanatan Kogi Ta Gabas

Sanata Jibrin Ya Musanta Janyewa Daga Takarar Sanatan Kogi Ta Gabas

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.