A ranar Talata ne Shugabar kamfanin jaridar LEADERSHIP Zainab Nda-Isaiah da Babban Editan Jaridar Mista Azu Ishiekwene suka karɓi lambar girmamawa daga ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa reshen Babban Birnin Taratyya Abuja.
A jawabin ta, Shugabar Jaridar LEADERSHIP, Zainab Nda-Isaiah, ta yaba da tsayin daka, jajircewa da kuma ƙwarewar ƴan jaridan Nijeriya, inda ta bayyana jajircewarsu a matsayin wani ginshiƙi na ɗorewar demokuraɗiyya, duk da cewa; suna gudanar da aikin nasu cikin yanayi mai matuƙar wahala.
Ta gabatar da wannan yabo ne a ranar Talata a Abuja, yayin bikin makon manema labarai na ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa (NUJ), na 2026.
Da take magana a wajen taron ƙwararrun, Nda-Isaiah ta bayyana yadda ta samu kanta a shugabancin jaridar LEADERSHIP, inda ta bayyana cewa; ta ɗauki gagarumin nauyi tun a farko, wanda ba ta taɓa tsammanin ɗauka ba.
Ta ce: “Tafiya ce wadda kawai ta zo min ɓagatatan, wadda kuma dole ne na sanya takalmin, wanda ko da wasa ban taɓa tsammanin zan iya sanyawa ba,” in ji ta.
Kazalika, ta danganta ci gaban kafafen yaɗa labaru da jajircewar ƴan jarida da kuma ƙwararrun, waɗanda a cewarta; suke jajircewa wajen ganin cewa, “duk abin da Nijeriya ta samar, za mu faɗa, ta hanyar jin muryoyinmu.”
Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida, a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin siyasa daban-daban.
Haka zalika, ta yaba wa ƴan jaridar, sakamakon kiyaye mutuncin sana’ar da kuma ci gaba da faɗin gaskiya ga masu mulki, duk kuwa da kasadar da ke tattare da yin hakan.
Ta kuma ƙara da cewa, ƴan jarida sukan yi aiki a wurare masu matuƙar haɗari, musamman ta fuskar faɗin gaskiya, amma duk da haka suna ci gaba da kiyaye ƙa’idojin da kuma yin kula a cikin rahotannin da suke bayarwa.
Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin ƴan siyasa daban-daban.
Shugabar Jaridar LEADERSHIP ɗin, ta kuma yaba wa manyan ƴan jarida, ciki har da Babban Editan Jaridar, Mista Azu, wanda ta bayyana a matsayin ginshiƙin bayar da tallafi, wanda jajircewarsa take taimaka wa ƙungiyar.
“Ba zan iya bayyana irin tallafi da gudunmawar da shi kansa da sauran mutanen da ke wannan kamfani na LEADERSHIP suka bayar ba, shi ya sa har yanzu muke tsaye da ƙafafunmu,” in ji ta.
Nda-Isaiah, wacce ta yarda da cewa; ita ba ƙwararriyar ƴar jarida ba ce, amma kuma ta dangantakar danginta da wannan aiki na jarida, inda ta bayyana shi a matsayin sana’a mai tushe da sha’awa da kuma gado.
A ƙarshe, ta bayyana godiyarta ga ƴan jarida, kan ci gaba da yi wa ƙasa hidima, inda ta ce; tsayin daka da sadaukarwar da suke bayarwa ta sa sana’ar take ci gaba da wanzuwa tsawon zamani.















Discussion about this post