ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar NUJ Ta Karrama Shugaba Da Babban Editan Kamfanin LEADERSHIP A Abuja

by Sani Anwar
2 weeks ago

A ranar Talata ne Shugabar kamfanin jaridar LEADERSHIP Zainab Nda-Isaiah da Babban Editan Jaridar Mista Azu Ishiekwene suka karɓi lambar girmamawa daga ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa reshen Babban Birnin Taratyya Abuja.

A jawabin ta, Shugabar Jaridar LEADERSHIP, Zainab Nda-Isaiah, ta yaba da tsayin daka, jajircewa da kuma ƙwarewar ƴan jaridan Nijeriya, inda ta bayyana jajircewarsu a matsayin wani ginshiƙi na ɗorewar demokuraɗiyya, duk da cewa; suna gudanar da aikin nasu cikin yanayi mai matuƙar wahala.

Ta gabatar da wannan yabo ne a ranar Talata a Abuja, yayin bikin makon manema labarai na ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa (NUJ), na 2026.

ADVERTISEMENT

Da take magana a wajen taron ƙwararrun, Nda-Isaiah ta bayyana yadda ta samu kanta a shugabancin jaridar LEADERSHIP, inda ta bayyana cewa; ta ɗauki gagarumin nauyi tun a farko, wanda ba ta taɓa tsammanin ɗauka ba.

Ta ce: “Tafiya ce wadda kawai ta zo min ɓagatatan, wadda kuma dole ne na sanya takalmin, wanda ko da wasa ban taɓa tsammanin zan iya sanyawa ba,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Kazalika, ta danganta ci gaban kafafen yaɗa labaru da jajircewar ƴan jarida da kuma ƙwararrun, waɗanda a cewarta; suke jajircewa wajen ganin cewa, “duk abin da Nijeriya ta samar, za mu faɗa, ta hanyar jin muryoyinmu.”

Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida, a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin siyasa daban-daban.

Haka zalika, ta yaba wa ƴan jaridar, sakamakon kiyaye mutuncin sana’ar da kuma ci gaba da faɗin gaskiya ga masu mulki, duk kuwa da kasadar da ke tattare da yin hakan.

Ta kuma ƙara da cewa, ƴan jarida sukan yi aiki a wurare masu matuƙar haɗari, musamman ta fuskar faɗin gaskiya, amma duk da haka suna ci gaba da kiyaye ƙa’idojin  da kuma yin kula a cikin rahotannin da suke bayarwa.

Nda-Isaiah ta bayyana yanayin gudanar da aikin ƴan jarida a matsayin mai matuƙar ƙalubale, inda ta yi nuni da cewa; har yanzu kafafen yaɗa labarai na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga gwamnatocin ƴan siyasa daban-daban.

Shugabar Jaridar LEADERSHIP ɗin, ta kuma yaba wa manyan ƴan jarida, ciki har da Babban Editan Jaridar, Mista Azu, wanda ta bayyana a matsayin ginshiƙin bayar da tallafi, wanda jajircewarsa take taimaka wa ƙungiyar.

“Ba zan iya bayyana irin tallafi da gudunmawar da shi kansa da sauran mutanen da ke wannan kamfani na LEADERSHIP suka bayar ba, shi ya sa har yanzu muke tsaye da ƙafafunmu,” in ji ta.

Nda-Isaiah, wacce ta yarda da cewa; ita ba ƙwararriyar ƴar jarida ba ce, amma kuma ta dangantakar danginta da wannan aiki na jarida, inda ta bayyana shi a matsayin sana’a mai tushe da sha’awa da kuma gado.

A ƙarshe, ta bayyana godiyarta ga ƴan jarida, kan ci gaba da yi wa ƙasa hidima, inda ta ce; tsayin daka da sadaukarwar da suke bayarwa ta sa sana’ar take ci gaba da wanzuwa tsawon zamani.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Sanata Jibrin Ya Musanta Janyewa Daga Takarar Sanatan Kogi Ta Gabas

Sanata Jibrin Ya Musanta Janyewa Daga Takarar Sanatan Kogi Ta Gabas

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.