Sanata mai wakiltar Kogi ta Gabas, Isah Jibrin, ya musanta rahotannin da ke cewa ya amince da janye kansa daga takarar sanata a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC gabanin zaɓen 2027, yana mai bayyana rahotannin a matsayin ƙarya da siyasar yaudara.
A wata sanarwa da ya fitar a Abuja, Sanatan ya ce har yanzu yana nan daram cikin takara kuma bai taɓa janye kansa ko ba wa wani izinin yin magana a madadinsa kan batun siyasa ba, yana zargin wasu ‘yan siyasa da ƙirƙirar labaran domin rikita APC a Kogi ta Gabas.
Ya jaddada cewa shi ne sahihin ɗan takarar APC a yankin kuma yana shirye fiye da kowane lokaci domin neman amincewar al’umma a karo na gaba. Haka kuma ya buƙaci shugabannin jam’iyya da magoya baya da su yi watsi da abin da ya kira farfaganda da yaɗa ƙarya daga masu neman haddasa rikici a cikin jam’iyyar.















Discussion about this post