Sabon rikici ya sake kunno kai a cikin Jam’iyyar APC a jihar Kaduna bayan Sanata Shehu Sani ya yi wa tsohon kakakin majalisar dokokin Jihar Kaduna Yusuf Ibrahim Zailani shaguɓe, inda ya kalubalance shi da ya fice daga jam’iyyar idan har yana da karfin siyasa da magoya bayan da zai iya cin zabe da su.
Sanata Shehu Sani ya bayyana hakan ne ranar Juma’a yayin da al’ummar Tudun Nupawa suka kai masa ziyarar gaisuwar Sallah a gidansa, inda ya yi dogon jawabi kan rikicin cikin gida da ya biyo bayan zaben fidda gwani na APC.
Shehu Sani ya ce tun bayan da Zailani ya sha kaye a zaben fidda gwani, ya koma amfani da kafafen sada zumunta wajen furta kalamai marasa tushe domin nuna fushinsa kan matakin da jam’iyyar ta dauka. “Idan yana ganin yana da karfi sosai a siyasa, ya kamata ya fita daga APC ya shiga wata jam’iyya domin auna farin jininsa a wajen zabe,” in ji Sanatan.
Ya kuma yi zargin cewa, Zailani na yawan amfani da sunan kusancinsa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen razana mutane da neman tausayi da goyon bayan siyasa.















Discussion about this post