ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Majalisar Dokokin Amurka Da Na Nijeriya Sun Gudanar Da Taro Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Amurka

A ranar Talata a Washington DC, da kwamitocin Majalisar Dokokin Amurka sun gudanar da taron haɗin gwiwa kan sace-sacen da ake yi da kuma zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

An gudanar da zaman ne bisa umarnin Shugaba Donald Trump, wanda a ranar 31 ga Oktoba ya umurci Kwamitin Kuɗin Gida na Majalisar Wakilai da ya binciki abin da ya bayyana a matsayin kisan Kiristoci a Nijeriya, sannan ya miƙa rahotonsu zuwa Fadar White House.

A gefe guda, Majalisar Wakilai ta Nijeriya za ta tattauna kan halin tsaro a ƙasar.

ADVERTISEMENT
  • Ci Gaban Fasahar AI A Kasar Sin Ya Nuna Gazawar Matakan Amurka Na Tare Hanyar Sin
  • Ƴan Ta’adda Sun Sace Mata Manoma 13 A Borno

Zaman Majalisar Amurka, wanda Mataimakin Shugaban Kwamitin Kuɗin Gida da Shugaban Ƙaramin Kwamitin Tsaro na Ƙasa Mario Díaz-Balart ya jagoranta, ya haɗa mambobin Kwamitin Kuɗin Gida da Kwamitin Harkokin Waje na Majalisar Wakilai tare da ƙwararru kan ’yancin addini.

Cikin mahalarta taron sun haɗa da ’Yan Majalisa Robert Aderholt, Riley Moore, Brian Mast, Chris Smith, Shugabar Kwamitin ’Yancin Addini na Duniya na Amurka, Ɓicky Hartzler, Sean Nelson na Ƙungiyar Alliance Defending Freedom International, da Dr Ebenezer Obadare na Hukumar Hulɗa da Harkokin Waje.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Díaz-Balart ya fara taron da bayyana ’yancin addini a duniya a matsayin “wajibi na ɗabi’a da kuma muhimmin abin da Amurka ke buƙata.” Ya jaddada cewa “bai kamata kowa ya ji tsaro rayuwarsa don ya zaɓai yadda zai gudanar da ibada ba.”

Ya ce “ Yana da niyyar ci gaba da tsara manufofi da za su kare ’yancin mutum na rayuwa bisa addininsa ba tare da tsoro na tashin hankali ko ramuwar gayya ba.”

Díaz-Balart ya lura cewa kuɗin da aka ware a dokar kasafin kuɗi ta FY26 yana magance wannan alƙawari, kuma ya ƙara da cewa yana shirin ƙarfafa waɗannan ƙoƙarin ta hanyar wucewa da matakin kasafin kuɗi na shekara ɗaya, wanda ya bayyana a matsayi muhimmi wajen ci gaba da aiwatar da manufofin ‘America First’.

Aderholt ya nuna damuwarsa, inda ya bayyana halin da ake ciki a Nijeriya a matsayin “rikici da ba za a iya yin watsi da shi ba.”

Ya ce, “Dole ne mu tsaya tsayin daka tare da al’ummomin Kiristoci na Nijeriya da duk masu bin addini da ake zalunta a duniya baki ɗaya, kuma ina yaba wa ƙoƙarin haɗin gwiwarmu wajen ba Shugaba bayanan da ake buƙata don tunkarar wannan masifa mai ƙaruwa.”

Moore ya danganta taron da sabuwar sanarwar gwamnatin kan sake sanya Nijeriya a matsayin ƙasa mai damuwa ta musamman.

Ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya da ta “ƙwace makaman waɗannan rundunonin, mayar da iyalan da aka tilasta musu barin gidajensu, sannan a gurfanar da masu laifin gaban shari’a.”

A jawabinsa, Shugaban Ƙaramin Kwamitin Harkokin Waje na Afirka na Majalisar Wakilai, Smith, ya bayyana Nijeriya a matsayin “Cibiya ta tashin hankalin addini,” yana cewa Kiristoci da Musulmai masu matsakaicin ra’ayi suna fuskantar “Barazanar kisa, fyaɗe, da azabtarwa a kowane lokaci.”

Amurka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Firaministan Sin Zai Gudanar Da Tattaunawa Ta “1+10” Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arziki Na Duniya

Firaministan Sin Zai Gudanar Da Tattaunawa Ta "1+10" Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arziki Na Duniya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.