ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Majalisar Dokokin Amurka Da Na Nijeriya Sun Gudanar Da Taro Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Amurka

A ranar Talata a Washington DC, da kwamitocin Majalisar Dokokin Amurka sun gudanar da taron haɗin gwiwa kan sace-sacen da ake yi da kuma zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

An gudanar da zaman ne bisa umarnin Shugaba Donald Trump, wanda a ranar 31 ga Oktoba ya umurci Kwamitin Kuɗin Gida na Majalisar Wakilai da ya binciki abin da ya bayyana a matsayin kisan Kiristoci a Nijeriya, sannan ya miƙa rahotonsu zuwa Fadar White House.

A gefe guda, Majalisar Wakilai ta Nijeriya za ta tattauna kan halin tsaro a ƙasar.

ADVERTISEMENT
  • Ci Gaban Fasahar AI A Kasar Sin Ya Nuna Gazawar Matakan Amurka Na Tare Hanyar Sin
  • Ƴan Ta’adda Sun Sace Mata Manoma 13 A Borno

Zaman Majalisar Amurka, wanda Mataimakin Shugaban Kwamitin Kuɗin Gida da Shugaban Ƙaramin Kwamitin Tsaro na Ƙasa Mario Díaz-Balart ya jagoranta, ya haɗa mambobin Kwamitin Kuɗin Gida da Kwamitin Harkokin Waje na Majalisar Wakilai tare da ƙwararru kan ’yancin addini.

Cikin mahalarta taron sun haɗa da ’Yan Majalisa Robert Aderholt, Riley Moore, Brian Mast, Chris Smith, Shugabar Kwamitin ’Yancin Addini na Duniya na Amurka, Ɓicky Hartzler, Sean Nelson na Ƙungiyar Alliance Defending Freedom International, da Dr Ebenezer Obadare na Hukumar Hulɗa da Harkokin Waje.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Díaz-Balart ya fara taron da bayyana ’yancin addini a duniya a matsayin “wajibi na ɗabi’a da kuma muhimmin abin da Amurka ke buƙata.” Ya jaddada cewa “bai kamata kowa ya ji tsaro rayuwarsa don ya zaɓai yadda zai gudanar da ibada ba.”

Ya ce “ Yana da niyyar ci gaba da tsara manufofi da za su kare ’yancin mutum na rayuwa bisa addininsa ba tare da tsoro na tashin hankali ko ramuwar gayya ba.”

Díaz-Balart ya lura cewa kuɗin da aka ware a dokar kasafin kuɗi ta FY26 yana magance wannan alƙawari, kuma ya ƙara da cewa yana shirin ƙarfafa waɗannan ƙoƙarin ta hanyar wucewa da matakin kasafin kuɗi na shekara ɗaya, wanda ya bayyana a matsayi muhimmi wajen ci gaba da aiwatar da manufofin ‘America First’.

Aderholt ya nuna damuwarsa, inda ya bayyana halin da ake ciki a Nijeriya a matsayin “rikici da ba za a iya yin watsi da shi ba.”

Ya ce, “Dole ne mu tsaya tsayin daka tare da al’ummomin Kiristoci na Nijeriya da duk masu bin addini da ake zalunta a duniya baki ɗaya, kuma ina yaba wa ƙoƙarin haɗin gwiwarmu wajen ba Shugaba bayanan da ake buƙata don tunkarar wannan masifa mai ƙaruwa.”

Moore ya danganta taron da sabuwar sanarwar gwamnatin kan sake sanya Nijeriya a matsayin ƙasa mai damuwa ta musamman.

Ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya da ta “ƙwace makaman waɗannan rundunonin, mayar da iyalan da aka tilasta musu barin gidajensu, sannan a gurfanar da masu laifin gaban shari’a.”

A jawabinsa, Shugaban Ƙaramin Kwamitin Harkokin Waje na Afirka na Majalisar Wakilai, Smith, ya bayyana Nijeriya a matsayin “Cibiya ta tashin hankalin addini,” yana cewa Kiristoci da Musulmai masu matsakaicin ra’ayi suna fuskantar “Barazanar kisa, fyaɗe, da azabtarwa a kowane lokaci.”

Amurka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Firaministan Sin Zai Gudanar Da Tattaunawa Ta “1+10” Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arziki Na Duniya

Firaministan Sin Zai Gudanar Da Tattaunawa Ta "1+10" Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arziki Na Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.