ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Majalisar Dokokin Amurka Da Na Nijeriya Sun Gudanar Da Taro Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Amurka

A ranar Talata a Washington DC, da kwamitocin Majalisar Dokokin Amurka sun gudanar da taron haɗin gwiwa kan sace-sacen da ake yi da kuma zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya.

An gudanar da zaman ne bisa umarnin Shugaba Donald Trump, wanda a ranar 31 ga Oktoba ya umurci Kwamitin Kuɗin Gida na Majalisar Wakilai da ya binciki abin da ya bayyana a matsayin kisan Kiristoci a Nijeriya, sannan ya miƙa rahotonsu zuwa Fadar White House.

A gefe guda, Majalisar Wakilai ta Nijeriya za ta tattauna kan halin tsaro a ƙasar.

ADVERTISEMENT
  • Ci Gaban Fasahar AI A Kasar Sin Ya Nuna Gazawar Matakan Amurka Na Tare Hanyar Sin
  • Ƴan Ta’adda Sun Sace Mata Manoma 13 A Borno

Zaman Majalisar Amurka, wanda Mataimakin Shugaban Kwamitin Kuɗin Gida da Shugaban Ƙaramin Kwamitin Tsaro na Ƙasa Mario Díaz-Balart ya jagoranta, ya haɗa mambobin Kwamitin Kuɗin Gida da Kwamitin Harkokin Waje na Majalisar Wakilai tare da ƙwararru kan ’yancin addini.

Cikin mahalarta taron sun haɗa da ’Yan Majalisa Robert Aderholt, Riley Moore, Brian Mast, Chris Smith, Shugabar Kwamitin ’Yancin Addini na Duniya na Amurka, Ɓicky Hartzler, Sean Nelson na Ƙungiyar Alliance Defending Freedom International, da Dr Ebenezer Obadare na Hukumar Hulɗa da Harkokin Waje.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Díaz-Balart ya fara taron da bayyana ’yancin addini a duniya a matsayin “wajibi na ɗabi’a da kuma muhimmin abin da Amurka ke buƙata.” Ya jaddada cewa “bai kamata kowa ya ji tsaro rayuwarsa don ya zaɓai yadda zai gudanar da ibada ba.”

Ya ce “ Yana da niyyar ci gaba da tsara manufofi da za su kare ’yancin mutum na rayuwa bisa addininsa ba tare da tsoro na tashin hankali ko ramuwar gayya ba.”

Díaz-Balart ya lura cewa kuɗin da aka ware a dokar kasafin kuɗi ta FY26 yana magance wannan alƙawari, kuma ya ƙara da cewa yana shirin ƙarfafa waɗannan ƙoƙarin ta hanyar wucewa da matakin kasafin kuɗi na shekara ɗaya, wanda ya bayyana a matsayi muhimmi wajen ci gaba da aiwatar da manufofin ‘America First’.

Aderholt ya nuna damuwarsa, inda ya bayyana halin da ake ciki a Nijeriya a matsayin “rikici da ba za a iya yin watsi da shi ba.”

Ya ce, “Dole ne mu tsaya tsayin daka tare da al’ummomin Kiristoci na Nijeriya da duk masu bin addini da ake zalunta a duniya baki ɗaya, kuma ina yaba wa ƙoƙarin haɗin gwiwarmu wajen ba Shugaba bayanan da ake buƙata don tunkarar wannan masifa mai ƙaruwa.”

Moore ya danganta taron da sabuwar sanarwar gwamnatin kan sake sanya Nijeriya a matsayin ƙasa mai damuwa ta musamman.

Ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya da ta “ƙwace makaman waɗannan rundunonin, mayar da iyalan da aka tilasta musu barin gidajensu, sannan a gurfanar da masu laifin gaban shari’a.”

A jawabinsa, Shugaban Ƙaramin Kwamitin Harkokin Waje na Afirka na Majalisar Wakilai, Smith, ya bayyana Nijeriya a matsayin “Cibiya ta tashin hankalin addini,” yana cewa Kiristoci da Musulmai masu matsakaicin ra’ayi suna fuskantar “Barazanar kisa, fyaɗe, da azabtarwa a kowane lokaci.”

Amurka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Firaministan Sin Zai Gudanar Da Tattaunawa Ta “1+10” Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arziki Na Duniya

Firaministan Sin Zai Gudanar Da Tattaunawa Ta "1+10" Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arziki Na Duniya

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.