ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Fashi da Makami A Abuja, Sun Kama Wani Mutum

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta daƙile wani yunƙurin fashi da makami a yankin Kado na Abuja, inda ta kama mutum ɗaya tare da ƙwato makamai da wasu kayayyakin da ake zargi na masu laifi.

A wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar a ranar Litinin, ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:15 na safiyar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026. Ta bayyana cewa ofishin ƴansanda na Mabushi ya samu kiran gaggawa cewa ƴan fashi na kai wa direbobi hari a kusa da gidan mai na MRS da ke Kado, lamarin da ya sa ƴansanda suka gaggauta kai ɗauki.

  • Hukumar FCTA Ta Fatattaki Mabarata 607 Daga Titunan Abuja
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Adeh ta ce da zarar jami’an suka isa wurin, waɗanda ake zargin su kusan uku ne, sun yi ƙoƙarin tserewa bayan sun hango ƴansanda, abin da ya haifar da artabu da musayar harbe-harbe. “A yayin wannan artabu, ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi ya samu raunin harbin bindiga kuma aka kai shi asibiti domin jinya, yayin da sauran suka tsere zuwa dazuka da ke kusa,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT

Ƴansanda sun tabbatar da cewa sun ƙwato abubuwa da dama daga wurin, ciki har da motar da ake zargin masu laifin ke amfani da ita. Daga cikin kayan da aka samu akwai mota kirar Volkswagen Golf 2 mai launin baƙi mai lambar rajista JJJ 112 DW, da bindigar Barreta guda daya, da bindiga ƙirar gida guda ɗaya, da janareta ƙirar Firman, da wayoyin hannu biyu, da katin ATM na Access Bank, da wasu kayayyaki kamar danƙon harbi (catapult), fensir na karfe (pliers), takalma, huluna da wasu kayan sawa.

Ta kara da cewa rundunar na ci gaba da farautar sauran wadanda suka tsere, tare da tabbatar da kudurin Kwamishinan ’Yan Sanda na FCT, CP Miller G. Dantawaye, na kare rayuka da dukiyoyin al’ummar babban birnin. Haka kuma, ’yan sanda sun bukaci mazauna Abuja da su kasance masu sa ido tare da kai rahoton duk wani abu da suka ga yana da shakku ta hanyar layukan gaggawa na rundunar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

Ƴansanda
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
  • Abubakar Sulaiman
    Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Ƴansanda
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.