ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Fashi da Makami A Abuja, Sun Kama Wani Mutum

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta daƙile wani yunƙurin fashi da makami a yankin Kado na Abuja, inda ta kama mutum ɗaya tare da ƙwato makamai da wasu kayayyakin da ake zargi na masu laifi.

A wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar a ranar Litinin, ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:15 na safiyar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026. Ta bayyana cewa ofishin ƴansanda na Mabushi ya samu kiran gaggawa cewa ƴan fashi na kai wa direbobi hari a kusa da gidan mai na MRS da ke Kado, lamarin da ya sa ƴansanda suka gaggauta kai ɗauki.

  • Hukumar FCTA Ta Fatattaki Mabarata 607 Daga Titunan Abuja
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Adeh ta ce da zarar jami’an suka isa wurin, waɗanda ake zargin su kusan uku ne, sun yi ƙoƙarin tserewa bayan sun hango ƴansanda, abin da ya haifar da artabu da musayar harbe-harbe. “A yayin wannan artabu, ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi ya samu raunin harbin bindiga kuma aka kai shi asibiti domin jinya, yayin da sauran suka tsere zuwa dazuka da ke kusa,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT

Ƴansanda sun tabbatar da cewa sun ƙwato abubuwa da dama daga wurin, ciki har da motar da ake zargin masu laifin ke amfani da ita. Daga cikin kayan da aka samu akwai mota kirar Volkswagen Golf 2 mai launin baƙi mai lambar rajista JJJ 112 DW, da bindigar Barreta guda daya, da bindiga ƙirar gida guda ɗaya, da janareta ƙirar Firman, da wayoyin hannu biyu, da katin ATM na Access Bank, da wasu kayayyaki kamar danƙon harbi (catapult), fensir na karfe (pliers), takalma, huluna da wasu kayan sawa.

Ta kara da cewa rundunar na ci gaba da farautar sauran wadanda suka tsere, tare da tabbatar da kudurin Kwamishinan ’Yan Sanda na FCT, CP Miller G. Dantawaye, na kare rayuka da dukiyoyin al’ummar babban birnin. Haka kuma, ’yan sanda sun bukaci mazauna Abuja da su kasance masu sa ido tare da kai rahoton duk wani abu da suka ga yana da shakku ta hanyar layukan gaggawa na rundunar.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

Ƴansanda
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Next Post
Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.