ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Fashi da Makami A Abuja, Sun Kama Wani Mutum

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta daƙile wani yunƙurin fashi da makami a yankin Kado na Abuja, inda ta kama mutum ɗaya tare da ƙwato makamai da wasu kayayyakin da ake zargi na masu laifi.

A wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar a ranar Litinin, ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:15 na safiyar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026. Ta bayyana cewa ofishin ƴansanda na Mabushi ya samu kiran gaggawa cewa ƴan fashi na kai wa direbobi hari a kusa da gidan mai na MRS da ke Kado, lamarin da ya sa ƴansanda suka gaggauta kai ɗauki.

  • Hukumar FCTA Ta Fatattaki Mabarata 607 Daga Titunan Abuja
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Adeh ta ce da zarar jami’an suka isa wurin, waɗanda ake zargin su kusan uku ne, sun yi ƙoƙarin tserewa bayan sun hango ƴansanda, abin da ya haifar da artabu da musayar harbe-harbe. “A yayin wannan artabu, ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi ya samu raunin harbin bindiga kuma aka kai shi asibiti domin jinya, yayin da sauran suka tsere zuwa dazuka da ke kusa,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT

Ƴansanda sun tabbatar da cewa sun ƙwato abubuwa da dama daga wurin, ciki har da motar da ake zargin masu laifin ke amfani da ita. Daga cikin kayan da aka samu akwai mota kirar Volkswagen Golf 2 mai launin baƙi mai lambar rajista JJJ 112 DW, da bindigar Barreta guda daya, da bindiga ƙirar gida guda ɗaya, da janareta ƙirar Firman, da wayoyin hannu biyu, da katin ATM na Access Bank, da wasu kayayyaki kamar danƙon harbi (catapult), fensir na karfe (pliers), takalma, huluna da wasu kayan sawa.

Ta kara da cewa rundunar na ci gaba da farautar sauran wadanda suka tsere, tare da tabbatar da kudurin Kwamishinan ’Yan Sanda na FCT, CP Miller G. Dantawaye, na kare rayuka da dukiyoyin al’ummar babban birnin. Haka kuma, ’yan sanda sun bukaci mazauna Abuja da su kasance masu sa ido tare da kai rahoton duk wani abu da suka ga yana da shakku ta hanyar layukan gaggawa na rundunar.

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Ƴansanda
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro
  • Abubakar Sulaiman
    Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama
  • Abubakar Sulaiman
    NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

MASU ALAKA

Ƴansanda
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Ƴansanda
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Ƴansanda

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Ƴansanda

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Ƴansanda

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.