ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Majalisar APC Na Binuwe Sun Sha Alwashin Ƙuri’u Miliyan 1 Ga Tinubu A 2027

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
APC

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Tawagar jam’iyyar APC ta jihar Binuwe a Majalisar Tarayya ta bayyana aniyarta na tabbatar da ƙarin ƙuri’u miliyan ɗaya ga Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027, inda ta danganta wannan shiri da aikin yin rajistar intanet (e-registration) da sabunta rajistar mambobi domin faɗaɗa tushen jam’iyyar a faɗin jihar.

Hon. Philip Agbese, ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Ado/Okpokwu/Ogbadibo kuma kakakin tawagar APC ta Binuwe a Majalisa, ya bayyana hakan a Makurdi. Ya ce matakin na daga cikin shirin haɗa ƙarfi da ƙarfe da manyan jiga-jigan jam’iyyar, musamman ta hanyar aiki tare da wata kungiya ƙarƙashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, domin tabbatar da cewa mambobin jam’iyyar da aka tantance sun shiga cikin tsarin rajistar na intanet.

  • Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe
  • Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Agbese ya bayyana ƙwarin gwuiwar cewa haɗa tsarin Akume da aikin rajistar zai ƙara yawan mambobin APC a Binuwe sosai. “Ƙungiyar Akume kaɗai na da mambobi fiye da rabin miliyan da aka tantance, kuma a cikin kwanaki bakwai masu zuwa za mu shigar da dukkan sunayensu. Wannan zai ƙara yawan mambobin APC da aƙalla 500,000, kuma muna nufin samun ƙarin ƙuri’u miliyan ɗaya ga Shugaba Tinubu a zagayen zaɓe na gaba,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya yi kira ga mambobin APC a faɗin jihar da su ba da cikakken haɗin kai ga jami’an jam’iyya a matakin ƙananan hukumomi domin tabbatar da nasarar aikin rajistar, yana mai gargaɗi kan rarrabuwar kai da sakaci. Ya jaddada cewa jam’iyyar za ta mai da goyon bayan jama’a zuwa gagarumar nasarar zaɓe a 2027, tare da cewa APC a Benue na shirin dawowa da ƙarfi fiye da da.

APC
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
  • Abubakar Sulaiman
    Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Ganduje Ya Koma Abuja Daga Landan, APC Na Shirye-shiryen Karɓar Gwamnan Kano

Ganduje Ya Koma Abuja Daga Landan, APC Na Shirye-shiryen Karɓar Gwamnan Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.