ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɓarawo Ya Sace Motar Masarautar Bauchi 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
5 months ago
Bauchi

Wani ɓarawo ya fuskanci koma baya a ƙoƙarinsa na sace mota ƙirar Toyota Hilux mallakin Masarautar Bauchi.

 

Lamarin a faru ne a ranar 5 ga watan Janairu, yayin da wanda ake zargi da sace motar ya yi awun gaba da ita a lokacin da direban motar ya tsaya Domin yin fitsari a wani gidan mai.

ADVERTISEMENT
  • Harin Venezuela Ta’asa Ce Da Amurka Ke Tafkawa Tun Bayan Yakin Duniya Na Biyu
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Fashi Da Makami A Hanyar Abuja Zuwa Kaduna

Wani mai suna Buhari Musa Umar, daga masarautar Bauchi ya ankarar da ‘yansandan da ke sintiri a kan shataletalen hanyar Jos da ke Bauchi dangane da sace motar.

 

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

Musa ya yi bayanin cewa direban motar ya tsaya a gidan Man Inkiya da nufin kara mai ne a motar.

 

Direban motar ya yi bayanin cewa, yana kan hanyarsa ne ta zuwa Ganjuwa domin kai wani saƙon da Sarki ya aikesa.

 

Direban, bayan ya sha mai ya shiga bayan gida domin ya yi fitsari inda ɓarawon ya yi amfani da wannan damar wajen sace motar tare da arcewa da ita.

 

A sanarwar manema labarai a ranar Talata, Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya ce, bayan samun labarin faruwar lamarin cikin gaggawa jami’ansu suka kai ɗauki domin nemo motar.

 

Ya ƙara da cewa, jami’an tsaron sun samu nasarar kamo motar a layin Bayan Gari tare da cafke wanda ake zargin da sace motar.

 

SP Habib ya ƙara da cewa, a lokacin da ake yi wa wanda ake zargi da sace motar tambayoyi, ya amsa laifin da ake zarginsa da bakinsa.

 

Jami’in watsa labaran ya ƙara da cewa a kan ci gaba da gudanar da bincike, kuma da zarar aka kammala za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu domin ya fuskanci Shari’a daidai da laifinsa.

 

Har-ila-yau, Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya nanata aniyar hukumar na yin aiki tuƙuro domin kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.

 

A wani faifayin bidiyo an gano yadda jama’a suke ta bin ɓarawon da gudu a lokacin da ya ja motar da nufin tserewa da ita inda suka yi ta masa ihun ɓarawo ɓarawo, yayin da shi kuma ya yi ta jan motar da gudun tsiya da nufin arcewa.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya
  • Sulaiman
    Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”
  • Sulaiman
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
  • Sulaiman
    Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

MASU ALAKA

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

June 16, 2026
Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

June 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

June 16, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Ce Wajibi Ne A Kare Halastattun Muradunta A Venezuela

Kasar Sin Ta Ce Wajibi Ne A Kare Halastattun Muradunta A Venezuela

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

June 16, 2026
Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

June 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

June 16, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Hukuncin Kotu Kan Ba Da Umarnin Soke Rajistar ADC

June 16, 2026
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

June 15, 2026
Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.