• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnonin Arewa Sun Nuna Yunwarsu A Fili -Matasan Arewa A Kudu

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
2023: Gwamnonin Arewa Sun Nuna Yunwarsu A Fili -Matasan Arewa A Kudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa da ke yankin kudu ta nuna takaicinta kan halin ko-in-kula da gwamnonin arewa suke yi wa al’umma tare da nuna yunwansu a fili wajen ci gaba da zama a karagar mulki a 2023, wanda hakan ne ya nuna cewa babu shugabanni masu kishi a arewa.

Gamayyar Kungiyoyin Matsan Arewa da ke Kudancin Nijeriya a Jihar Legas ta kuma bukaci al’ummar arewacin Nijeriya su zabi cancanta su manta da batun biye wa jam’iyya a zaben 2023.

  • Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari’a Da Shigar Matsubbata

Shugaban gamayyar kungiyoyin matasan arewa a kudu, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci shi ya bayyana hakan a madadin ‘ya’yan kungiyar a wata sanarwar manema labarai da ya aike wa wakilinmu.
A cewar gamayyar, ta yi wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari kyakkyawan zato da fatan alkairi a zaben shekarar 2015, wanda har ta dunga sayen katin tana tura masa kuadade domin ya samu damar darewa a kan karagar mulki, amma kuma a halin yanzu dai arewa ta zama kushewa, inda ake ta kashe al’umma ba ji babu gani duk ka cewa dan arewa yake shugabancin kasar nan.

“Shugabanninmu na arewa su sani Allah ba ya zalunci, sannan kuma ba ya barin duk wani azzalumi a doran kasa, da yana bari ai da har yanzu Fir’auna na nan a doron kasa.

“Domin haka muna kira ga matasa da su guji bangar siyasa, domin babu ribar da za su samu. Wadanda ma suke yi wa bangar siyasar suna ganin ‘ya’yansu a wurin bangar siyasar, don haka wannan ya isa mai hankali ya yi karatun ta-natsu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

“Ana yi wa arewa mugun tanadi kuma wadanda ake ganin ya kamata su yi magana da su ma ake hada baki wajen yakarmu.
“Akwai arziki a yankin arewa mai dinbin yawa, tun daga kan zinari da lu’u-lu’u da sauran manyan ma’adanai, wanda shi ne dalilan da ya sa ake kashe mu, amma kuma a guji fushin takala, domin a halin yanzu talakawan arewa na cikin halin lahaula, sai Allah ya kyauta ya kawo mana dauki.”

Gamayyar Kungiyoyin Matsan Arewa da ke Kudancin Nijeriya ta dai bayyana cewa wannan sako ne ga dukkan matasan arewacin Nijeriya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi: Sin Za Ta Dauki Managartan Matakai Don Ci Gaba Da Tallafawa Ajandar Ci Gaba Mai Dorewa Ta MDD Nan Da 2030

Next Post

Ko Kun Taba Jin Labarin Dausayin Jinbianxi Na Birnin Zhangjiajie A Kasar Sin?

Related

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

48 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

2 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

4 hours ago
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba
Manyan Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

6 hours ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

6 hours ago
Next Post
Ko Kun Taba Jin Labarin Dausayin Jinbianxi Na Birnin Zhangjiajie A Kasar Sin?

Ko Kun Taba Jin Labarin Dausayin Jinbianxi Na Birnin Zhangjiajie A Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.