• Leadership Hausa
Thursday, August 18, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Bakon Marubuci

Yaro Tsaya Matsayinka: Ina Makomar Sha’aban Sharada A Siyasar Kano?

by Buhari Abba Rano
2 months ago
in Bakon Marubuci
0
Yaro Tsaya Matsayinka: Ina Makomar Sha’aban Sharada A Siyasar Kano?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A dai-dai lokacin da jam’iyyu a Nijeriya ke ƙoƙarin kammala zaɓukan fidda gwani domin miƙawa hukumar zaɓe ta ƙasa INEC sunayen waɗanda za su shiga babban zaɓen shekarar 2023.

Zamu ɗan yi taƙaitaccen nazari akan makomar siyasar ɗan majalisar wakilai mai wakilatar ƙaramar hukumar Birnin Kano a zauren majalisar wakilai, Sha’aban Ibrahim Sharada.

  • Zaben APC: Ragowar ‘Yan Takara Sun Yi Watsi Da Matakin Gwamnoni Na Ware Mutum 5
  • Gwamnonin APC Sun Kara Rage Adadin ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Daga 5 Zuwa 3

Sha’aban Ibrahim Sharada ya kasance ƙalilan daga cikin matasa a jihar Kano da su ka samu babbar dama a siyasa irin ta Najeriya, musamman idan aka yi la’akari da ƙananan shekarunsa da kuma muƙamin da ya fara da shi wato mai taimakawa shugaba Muhammadu Buhari kan harkokin watsa labarai wanda wannan ce ta ba shi damar samun takarar ɗan majalisar wakilai kuma ya yi nasara a zaɓen shekarar 2019, duk da irin ƙalubalen da ya fuskanta a cikin jam’iyyar APC reshen ƙaramar hukumar Birni.

Samun wannan nasara da Sha’aban ya yi ta sa ya samu damar kasancewa shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilan Najeriya. Tabbas wannan matashin ɗan siyasa ya samu dama fiye da wasu daga cikin takwarorinsa musamman waɗanda su ka fito daga jihar Kano.

Kamar yadda al’umma ke yiwa siyasar Kano kirari da cewa ‘Siyasar Kano Sai Kano’, wannan babu shakka haka abin ya ke domin sunan Sha’aban Sharada ya karaɗe da’irar siyasar Kano, musamman a shirye-shiryen siyasa da ake gabatarwa a jihar.

Labarai Masu Nasaba

A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)

Dambarwar Takarar Kujerar Gwamnan Kano A PDP

Duk da irin rikicin siyasar da ke tsakanin Sha’aban da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da tsohon Kwamishina Mukhtar Ishaq Yakasai da tsohon ɗan majalisar dokoki Dakta Baffa Babba Danagundi da shugaban ƙaramar hukumar Birni, Fa’izu Alfindiki, amma hakan bai sa gwiwar matashin ɗan siyasar ta yi sanyi a siyasance ba, domin tuni ya cika kafafen yaɗa labarai akan bayyana buƙatarsa ta yin takarar gwamnan Kano a jam’iyyar APC ba.

Irin ƙarfin hali da kuma tsiwar da Sha’aban ɗin ke yiwa jiga – jigan jam’iyyar APC a ƙaramar hukumar Birnin Kano, ya sanya ake masa laƙabi da SAURO Mai Hana Giwa Bacci. Kuma ga duk mai bibiyar siyasar Kano, ya ga matashin ɗan siyasar ya tayar da ƙura a cikin jam’iyyar APC, musamman a lokacin da ake shari’a mai nasaba da shugabanci a jam’iyyar.

Tabbas irin yadda kafafen yaɗa labarai na ciki da wajen Najeriya, su ka baiwa Sha’aban haɗin kai da kuma rawaito irin nasarar da tsaginsu na G7 ke samu akan Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya sanya ya ke ganin babu wani ɗan siyasa a gabansa a cikin jam’iyyar APC.

A ɗaya ɓangaren kuma Sha’aban ɗin ya tattara wasu matasa a cikin wata ƙungiya mai suna FITILAR Kano, da babban aikinsu shi ne kare muradinsa da kuma ganin bukatar sa ta biya ta hanyar tattara masa matasa da ba su horo kan ƙananan sana’o’in dogaro da kai a wasu daga cikin ƙananan hukumomi 44 da ke Kano.

Jami’yyar APC tana fara sayar da fom ɗin takara a dukkanin muƙamai, sai aka jiyo wata gamayyar ƙungiyar matasan da Sha’aban ɗin ya samawa shirin nan na gwamnatin tarayya mai laƙabin N- POWER, sun tara kuɗi kimanin Naira Miliyan 50 tare da siyawa Sauro ɗin fom ɗin takarar gwamnan Kano.

Wannan ce ta ba shi damar shiga zaɓen fidda gwani tsakaninsa da mataimakin gwamnan Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, inda Sha’aban Ibrahim Sharada, ya yi rashin nasara, wanda hakan ne ya bai wa tsohon Kwamishinan Ayyuka na musamman, Muntari Ishaq Yakasai damar samun tikitin takarar majalisar wakilai ta tarayya, a ƙarƙashin jam’iyya APC.

Gabanin fara zaɓen fidda gwanin Sha’aban Ibrahim Sharada ya gabatar da wani jawabi na mintuna 12 a gaban gwamna Abdullahi Umar Ganduje da duk wani mai ruwa da tsaki na jam’iyyar APC reshen jihar Kano, inda a nan aka ji Sauro ɗin ya tuba daga dukkanin irin tsiwar da ya yiwa manyan jam’iyyar tun daga kan Gwamna har zuwa kan shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kano, Fa’izu Alfindiki, tare kuma da sha alwashi akan zai karɓi sakamakon zaben fidda gwanin.

Sai dai wani abu mai kama da tufka da warwara da Sauro ɗin shi ne yadda aka jiyo shi ya ki amincewa da sakamakon zaben tare da rubutawa uwar jami’yyar ta ƙasa ƙorafi tare kuma da zargin da ɗan majalisar ya yi akan cewa an kashe masa magoya baya tare da jikkata waɗansu, sai dai jami’an ƴan sanda a Kano sun shaida wa manema labarai cewa babu rahoton rikici a yayin zaben balle a yi maganar hare-hare ko asarar rai, har aka kammala zaben.

Yanzu abin tambayar shi ne; Mecece makomar siyasar Sha’aban Ibrahim Sharada ɗin a fagen siyasar Kano? Ko zancen ƴan duniya ya ɗebi Sauro ya wuce matsayinsa?

Tags: kanoSha'aban SharadaSiyasar Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Badakalar Naira Biliyan 80: Cibiyar Ta Ce Akanta-janar Na kasa Da Aka Dakatar Ba Danta Bane

Next Post

Zaben APC: Yariman Bakura Ya Ce Bai Janye Wa Kowa Takararsa Ba

Related

A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)
Bakon Marubuci

A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)

4 weeks ago
Dambarwar Takarar Kujerar Gwamnan Kano A PDP
Bakon Marubuci

Dambarwar Takarar Kujerar Gwamnan Kano A PDP

1 month ago
Yaro
Bakon Marubuci

A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

2 months ago
12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra’ayin Najib Sani
Bakon Marubuci

12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra’ayin Najib Sani

2 months ago
Rage Raɗaɗin Fatara Ta Hanyar Ciyar Da ‘Yan Makaranta
Bakon Marubuci

Rage Raɗaɗin Fatara Ta Hanyar Ciyar Da ‘Yan Makaranta

3 months ago
Kisan ‘Yan Arewa A Kudu: An Bukaci Gwamnati Ta Gaggauta Daukar Mataki
Bakon Marubuci

Kisan ‘Yan Arewa A Kudu: An Bukaci Gwamnati Ta Gaggauta Daukar Mataki

3 months ago
Next Post
Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

Zaben APC: Yariman Bakura Ya Ce Bai Janye Wa Kowa Takararsa Ba

LABARAI MASU NASABA

Fada Ya Barke Tsakanin Shugabannin ’Yan Bindiga, 2 Sun Mutu Yayin Rikicin A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Shingen Bincike Na ‘Yan Sanda Sun Harbe Mutum 2 A Ebonyi

August 18, 2022
An Cafke Mutumin Da Zai Aike Da Bindigu Kano Daga Abuja Ta Tashar Mota

An Cafke Mutumin Da Zai Aike Da Bindigu Kano Daga Abuja Ta Tashar Mota

August 18, 2022
Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

Ku Yi Watsi Da Masu Wa’azin Son Wargaza Hadin Kan Nijeriya —IBB

August 18, 2022
Kungiyar Haɗin Kan Musulunci ta Duniya Ta Ziyarci Medina Baye Niass

Kungiyar Haɗin Kan Musulunci ta Duniya Ta Ziyarci Medina Baye Niass

August 18, 2022
Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

August 18, 2022
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman

Matawalle Ya Amince Da Hukuncin Kisa Kan Masu Garkuwa Da Masu Ba ‘Yan Bindiga Bayanan Sirri

August 17, 2022

Ma’aikatan Wutar Lantarki Sun Janye Yajin Aikin Da Suka Fara Na Mako 2

August 17, 2022
Kudin Shigar Manyan Kamfanonin Kera Na’urorin Sadarwa Na Sin Ya Kai Yuan Triliyan 14 A 2021

Kudin Shigar Manyan Kamfanonin Kera Na’urorin Sadarwa Na Sin Ya Kai Yuan Triliyan 14 A 2021

August 17, 2022
Yanayin Kare Hakkin Dan Adam Na ‘Yan Kananan Kabilun Sin Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Yanayin Kare Hakkin Dan Adam Na ‘Yan Kananan Kabilun Sin Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 17, 2022
Gaskiya Ba Ta Buya…

Gaskiya Ba Ta Buya…

August 17, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.