ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaro Tsaya Matsayinka: Ina Makomar Sha’aban Sharada A Siyasar Kano?

by Buhari Abba Rano
4 years ago
Yaro

A dai-dai lokacin da jam’iyyu a Nijeriya ke ƙoƙarin kammala zaɓukan fidda gwani domin miƙawa hukumar zaɓe ta ƙasa INEC sunayen waɗanda za su shiga babban zaɓen shekarar 2023.

Zamu ɗan yi taƙaitaccen nazari akan makomar siyasar ɗan majalisar wakilai mai wakilatar ƙaramar hukumar Birnin Kano a zauren majalisar wakilai, Sha’aban Ibrahim Sharada.

  • Zaben APC: Ragowar ‘Yan Takara Sun Yi Watsi Da Matakin Gwamnoni Na Ware Mutum 5
  • Gwamnonin APC Sun Kara Rage Adadin ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Daga 5 Zuwa 3

Sha’aban Ibrahim Sharada ya kasance ƙalilan daga cikin matasa a jihar Kano da su ka samu babbar dama a siyasa irin ta Najeriya, musamman idan aka yi la’akari da ƙananan shekarunsa da kuma muƙamin da ya fara da shi wato mai taimakawa shugaba Muhammadu Buhari kan harkokin watsa labarai wanda wannan ce ta ba shi damar samun takarar ɗan majalisar wakilai kuma ya yi nasara a zaɓen shekarar 2019, duk da irin ƙalubalen da ya fuskanta a cikin jam’iyyar APC reshen ƙaramar hukumar Birni.

ADVERTISEMENT

Samun wannan nasara da Sha’aban ya yi ta sa ya samu damar kasancewa shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilan Najeriya. Tabbas wannan matashin ɗan siyasa ya samu dama fiye da wasu daga cikin takwarorinsa musamman waɗanda su ka fito daga jihar Kano.

Kamar yadda al’umma ke yiwa siyasar Kano kirari da cewa ‘Siyasar Kano Sai Kano’, wannan babu shakka haka abin ya ke domin sunan Sha’aban Sharada ya karaɗe da’irar siyasar Kano, musamman a shirye-shiryen siyasa da ake gabatarwa a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

Duk da irin rikicin siyasar da ke tsakanin Sha’aban da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da tsohon Kwamishina Mukhtar Ishaq Yakasai da tsohon ɗan majalisar dokoki Dakta Baffa Babba Danagundi da shugaban ƙaramar hukumar Birni, Fa’izu Alfindiki, amma hakan bai sa gwiwar matashin ɗan siyasar ta yi sanyi a siyasance ba, domin tuni ya cika kafafen yaɗa labarai akan bayyana buƙatarsa ta yin takarar gwamnan Kano a jam’iyyar APC ba.

Irin ƙarfin hali da kuma tsiwar da Sha’aban ɗin ke yiwa jiga – jigan jam’iyyar APC a ƙaramar hukumar Birnin Kano, ya sanya ake masa laƙabi da SAURO Mai Hana Giwa Bacci. Kuma ga duk mai bibiyar siyasar Kano, ya ga matashin ɗan siyasar ya tayar da ƙura a cikin jam’iyyar APC, musamman a lokacin da ake shari’a mai nasaba da shugabanci a jam’iyyar.

Tabbas irin yadda kafafen yaɗa labarai na ciki da wajen Najeriya, su ka baiwa Sha’aban haɗin kai da kuma rawaito irin nasarar da tsaginsu na G7 ke samu akan Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya sanya ya ke ganin babu wani ɗan siyasa a gabansa a cikin jam’iyyar APC.

A ɗaya ɓangaren kuma Sha’aban ɗin ya tattara wasu matasa a cikin wata ƙungiya mai suna FITILAR Kano, da babban aikinsu shi ne kare muradinsa da kuma ganin bukatar sa ta biya ta hanyar tattara masa matasa da ba su horo kan ƙananan sana’o’in dogaro da kai a wasu daga cikin ƙananan hukumomi 44 da ke Kano.

Jami’yyar APC tana fara sayar da fom ɗin takara a dukkanin muƙamai, sai aka jiyo wata gamayyar ƙungiyar matasan da Sha’aban ɗin ya samawa shirin nan na gwamnatin tarayya mai laƙabin N- POWER, sun tara kuɗi kimanin Naira Miliyan 50 tare da siyawa Sauro ɗin fom ɗin takarar gwamnan Kano.

Wannan ce ta ba shi damar shiga zaɓen fidda gwani tsakaninsa da mataimakin gwamnan Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, inda Sha’aban Ibrahim Sharada, ya yi rashin nasara, wanda hakan ne ya bai wa tsohon Kwamishinan Ayyuka na musamman, Muntari Ishaq Yakasai damar samun tikitin takarar majalisar wakilai ta tarayya, a ƙarƙashin jam’iyya APC.

Gabanin fara zaɓen fidda gwanin Sha’aban Ibrahim Sharada ya gabatar da wani jawabi na mintuna 12 a gaban gwamna Abdullahi Umar Ganduje da duk wani mai ruwa da tsaki na jam’iyyar APC reshen jihar Kano, inda a nan aka ji Sauro ɗin ya tuba daga dukkanin irin tsiwar da ya yiwa manyan jam’iyyar tun daga kan Gwamna har zuwa kan shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kano, Fa’izu Alfindiki, tare kuma da sha alwashi akan zai karɓi sakamakon zaben fidda gwanin.

Sai dai wani abu mai kama da tufka da warwara da Sauro ɗin shi ne yadda aka jiyo shi ya ki amincewa da sakamakon zaben tare da rubutawa uwar jami’yyar ta ƙasa ƙorafi tare kuma da zargin da ɗan majalisar ya yi akan cewa an kashe masa magoya baya tare da jikkata waɗansu, sai dai jami’an ƴan sanda a Kano sun shaida wa manema labarai cewa babu rahoton rikici a yayin zaben balle a yi maganar hare-hare ko asarar rai, har aka kammala zaben.

Yanzu abin tambayar shi ne; Mecece makomar siyasar Sha’aban Ibrahim Sharada ɗin a fagen siyasar Kano? Ko zancen ƴan duniya ya ɗebi Sauro ya wuce matsayinsa?

Yaro
Buhari Abba Rano
+ postsBio
  • Buhari Abba Rano
    https://hausa.leadership.ng/author/buhari-abba-rano/
    2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?
  • Buhari Abba Rano
    https://hausa.leadership.ng/author/buhari-abba-rano/
    Ficewar Malam Shekarau Daga NNPP: Me Ya Sa Hankalin ‘Yan Kwankwasiyya Ya Tashi?

MASU ALAKA

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya
Bakon Marubuci

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

Zaben APC: Yariman Bakura Ya Ce Bai Janye Wa Kowa Takararsa Ba

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.