ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ADC Ta Nemi A Binciki Zargin Kwashe Naira Biliyan 800 Daga FAAC Wajen Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu

by Sulaiman
2 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan zargin cewa gwamnoni na jam’iyyar APC mai mulki sun karkatar da kuɗaɗen da aka ware daga Asusun Raba Kuɗaɗen Tarayya (FAAC) domin tallafa wa yaƙin neman sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu gabanin zaɓen shekarar 2027.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Talata, ADC ta bayyana zargin karkatar da sama da naira biliyan 800 daga kuɗaɗen FAAC a matsayin “abin kunya, rashin tausayi da kuma babban laifi,” musamman a lokacin da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke fama da matsin tattalin arziki.

Jam’iyyar adawar ta ce zargin ya ƙara tabbatar da abin da mutane da dama suka daɗe suna zargi cewa yayin da gwamnati ke roƙon jama’a da su kara hakuri su jure radadin manufofin sauya tattalin arzikinta, ana zargin ana mayar da kuɗaɗen gwamnati zuwa asusun siyasa domin zaɓe mai zuwa.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, “A ƙarƙashin gwamnatin APC, jihohi na samun kuɗi fiye da kowane lokaci a tarihin Nijeriya, amma duk da haka ‘yan Nijeriya na ƙara talaucewa, yunwa da shiga halin ƙaƙa-ni-ka-yi. Hanyoyi na ci gaba da lalacewa. Asibitoci babu kayan aiki. Makarantu na fama da ƙarancin kuɗi. Ma’aikata ba sa samun isasshen albashi. Al’umma ba su da tsaro. Abu guda da ke ƙaruwa shi ne ƙwazon siyasar jam’iyya mai mulki kan yadda za ta sake lashe zaɓe mai zuwa”

ADC ta ce idan har zargin da jaridar THEWILL ta wallafa gaskiya ne, hakan ya zama “cin amana da kuma satar dukiyar al’ummar Nijeriya kai tsaye.”

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

“An ware kuɗaɗen FAAC ne domin samar da ci gaban al’umma, biyan albashi, kiwon lafiya, ilimi, gine-ginen more rayuwa, tsaro da walwalar jama’a, ba domin ɗaukar nauyin sake zaɓen mutum guda ba,” in ji sanarwar.

ADC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Zamfara

Sama Da Mutane 100 Sun Mutu A Harin Sama Da Aka Kai Kasuwar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.