Jam’iyyar ADC ta buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan zargin cewa gwamnoni na jam’iyyar APC mai mulki sun karkatar da kuɗaɗen da aka ware daga Asusun Raba Kuɗaɗen Tarayya (FAAC) domin tallafa wa yaƙin neman sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu gabanin zaɓen shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Talata, ADC ta bayyana zargin karkatar da sama da naira biliyan 800 daga kuɗaɗen FAAC a matsayin “abin kunya, rashin tausayi da kuma babban laifi,” musamman a lokacin da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke fama da matsin tattalin arziki.
Jam’iyyar adawar ta ce zargin ya ƙara tabbatar da abin da mutane da dama suka daɗe suna zargi cewa yayin da gwamnati ke roƙon jama’a da su kara hakuri su jure radadin manufofin sauya tattalin arzikinta, ana zargin ana mayar da kuɗaɗen gwamnati zuwa asusun siyasa domin zaɓe mai zuwa.
A cewar sanarwar, “A ƙarƙashin gwamnatin APC, jihohi na samun kuɗi fiye da kowane lokaci a tarihin Nijeriya, amma duk da haka ‘yan Nijeriya na ƙara talaucewa, yunwa da shiga halin ƙaƙa-ni-ka-yi. Hanyoyi na ci gaba da lalacewa. Asibitoci babu kayan aiki. Makarantu na fama da ƙarancin kuɗi. Ma’aikata ba sa samun isasshen albashi. Al’umma ba su da tsaro. Abu guda da ke ƙaruwa shi ne ƙwazon siyasar jam’iyya mai mulki kan yadda za ta sake lashe zaɓe mai zuwa”
ADC ta ce idan har zargin da jaridar THEWILL ta wallafa gaskiya ne, hakan ya zama “cin amana da kuma satar dukiyar al’ummar Nijeriya kai tsaye.”
“An ware kuɗaɗen FAAC ne domin samar da ci gaban al’umma, biyan albashi, kiwon lafiya, ilimi, gine-ginen more rayuwa, tsaro da walwalar jama’a, ba domin ɗaukar nauyin sake zaɓen mutum guda ba,” in ji sanarwar.















Discussion about this post