ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutane 100 Sun Mutu A Harin Sama Da Aka Kai Kasuwar Zamfara

by Sulaiman
1 month ago
Zamfara

Wani harin sama da sojoji suka kai kan kasuwar Tumfa da ke ƙaramar hukumar Zurmi a Jihar Zamfara ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 117 tare da jikkata wasu da dama. Mazauna yankin sun ce waɗanda suka mutu sun haɗa da ‘yan bindiga da mutanen yankin. In ji rahoton Daily Trust

An kai harin ne a ranar Lahadi, ranar da rundunar kuma ta kai makamancin wannan harin a Guradnayi, kusa da Kusasu a ƙaramar hukumar Shiroro ta Jihar Neja, inda ya kuma yi sanadiyyar mutuwar mutane mazauna yankin su 13.

Rahotannin harin da aka kai Tumfa sun bayyana ne a ƙarshen ranar Litinin saboda matsalar sadarwa a yankin.

ADVERTISEMENT

An ce Tumfa da wasu ƙauyukan da ke maƙwabtaka da ita a ƙaramar hukumar Zurmi na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga, inda mazauna yankin ke rayuwa tare da su saboda su ne suke da iko da yankin kamar hukumomin gwamnati.

Wani jagoran al’umma, Garba Ibrahim Mashema, ya ce har yanzu yana da wahala a tantance ainihin yawan waɗanda suka mutu a harin saman da aka kai kasuwar ranar Lahadi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

“A yanzu yana da wahala a tantance cikakken adadin waɗanda suka mutu. Kowa — mazauna gari da ‘yan bindiga — na zuwa kasuwar. Jama’a na rayuwa ne ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga, babu abin da za su iya yi,” in ji shi yayin tattaunawa da AFP.

Aliyu Musa, wani mazaunin garin Zurmi da ke kimanin kilomita bakwai daga Tumfa, ya ce da dama daga cikin waɗanda suka mutu ‘yan kasuwa ne da masu sayar da abinci, ciki har da ‘yan mata masu sayar da kunu da awara. Ya kiyasta yawan mace-macen zuwa 117.

“Gaskiya ne, kasuwar Tumfa na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga. Ita ce sansaninsu. Duk wanda ya je can ya san ya shiga yankinsu,” in ji Musa.

Wani ɗan uwan wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce jirgin yaƙin sojoji ya fara shawagi a saman kasuwar domin bincike kafin ya dawo bayan wasu sa’o’i ya kai harin bam.

Ya kuma ce wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar kamar Fakai, Mayasa da Mashema na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga saboda babu wata hukuma ta gwamnati a yankunan.

“Babu wata hukuma ta doka a ƙauyuka kamar Fakai, Mayasa da Mashema. ‘Yan bindiga ne suka zama alkalai da ‘yansanda,” in ji shi.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Ɗaliban Jami’ar Nasarawa da Aka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ɗaliban Jami’ar Nasarawa da Aka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.