ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutane 100 Sun Mutu A Harin Sama Da Aka Kai Kasuwar Zamfara

by Sulaiman
2 months ago
Zamfara

Wani harin sama da sojoji suka kai kan kasuwar Tumfa da ke ƙaramar hukumar Zurmi a Jihar Zamfara ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 117 tare da jikkata wasu da dama. Mazauna yankin sun ce waɗanda suka mutu sun haɗa da ‘yan bindiga da mutanen yankin. In ji rahoton Daily Trust

An kai harin ne a ranar Lahadi, ranar da rundunar kuma ta kai makamancin wannan harin a Guradnayi, kusa da Kusasu a ƙaramar hukumar Shiroro ta Jihar Neja, inda ya kuma yi sanadiyyar mutuwar mutane mazauna yankin su 13.

Rahotannin harin da aka kai Tumfa sun bayyana ne a ƙarshen ranar Litinin saboda matsalar sadarwa a yankin.

ADVERTISEMENT

An ce Tumfa da wasu ƙauyukan da ke maƙwabtaka da ita a ƙaramar hukumar Zurmi na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga, inda mazauna yankin ke rayuwa tare da su saboda su ne suke da iko da yankin kamar hukumomin gwamnati.

Wani jagoran al’umma, Garba Ibrahim Mashema, ya ce har yanzu yana da wahala a tantance ainihin yawan waɗanda suka mutu a harin saman da aka kai kasuwar ranar Lahadi.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

“A yanzu yana da wahala a tantance cikakken adadin waɗanda suka mutu. Kowa — mazauna gari da ‘yan bindiga — na zuwa kasuwar. Jama’a na rayuwa ne ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga, babu abin da za su iya yi,” in ji shi yayin tattaunawa da AFP.

Aliyu Musa, wani mazaunin garin Zurmi da ke kimanin kilomita bakwai daga Tumfa, ya ce da dama daga cikin waɗanda suka mutu ‘yan kasuwa ne da masu sayar da abinci, ciki har da ‘yan mata masu sayar da kunu da awara. Ya kiyasta yawan mace-macen zuwa 117.

“Gaskiya ne, kasuwar Tumfa na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga. Ita ce sansaninsu. Duk wanda ya je can ya san ya shiga yankinsu,” in ji Musa.

Wani ɗan uwan wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce jirgin yaƙin sojoji ya fara shawagi a saman kasuwar domin bincike kafin ya dawo bayan wasu sa’o’i ya kai harin bam.

Ya kuma ce wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar kamar Fakai, Mayasa da Mashema na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga saboda babu wata hukuma ta gwamnati a yankunan.

“Babu wata hukuma ta doka a ƙauyuka kamar Fakai, Mayasa da Mashema. ‘Yan bindiga ne suka zama alkalai da ‘yansanda,” in ji shi.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Ɗaliban Jami’ar Nasarawa da Aka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ɗaliban Jami’ar Nasarawa da Aka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.