ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutane 100 Sun Mutu A Harin Sama Da Aka Kai Kasuwar Zamfara

by Sulaiman
3 weeks ago
Zamfara

Wani harin sama da sojoji suka kai kan kasuwar Tumfa da ke ƙaramar hukumar Zurmi a Jihar Zamfara ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 117 tare da jikkata wasu da dama. Mazauna yankin sun ce waɗanda suka mutu sun haɗa da ‘yan bindiga da mutanen yankin. In ji rahoton Daily Trust

An kai harin ne a ranar Lahadi, ranar da rundunar kuma ta kai makamancin wannan harin a Guradnayi, kusa da Kusasu a ƙaramar hukumar Shiroro ta Jihar Neja, inda ya kuma yi sanadiyyar mutuwar mutane mazauna yankin su 13.

Rahotannin harin da aka kai Tumfa sun bayyana ne a ƙarshen ranar Litinin saboda matsalar sadarwa a yankin.

ADVERTISEMENT

An ce Tumfa da wasu ƙauyukan da ke maƙwabtaka da ita a ƙaramar hukumar Zurmi na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga, inda mazauna yankin ke rayuwa tare da su saboda su ne suke da iko da yankin kamar hukumomin gwamnati.

Wani jagoran al’umma, Garba Ibrahim Mashema, ya ce har yanzu yana da wahala a tantance ainihin yawan waɗanda suka mutu a harin saman da aka kai kasuwar ranar Lahadi.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“A yanzu yana da wahala a tantance cikakken adadin waɗanda suka mutu. Kowa — mazauna gari da ‘yan bindiga — na zuwa kasuwar. Jama’a na rayuwa ne ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga, babu abin da za su iya yi,” in ji shi yayin tattaunawa da AFP.

Aliyu Musa, wani mazaunin garin Zurmi da ke kimanin kilomita bakwai daga Tumfa, ya ce da dama daga cikin waɗanda suka mutu ‘yan kasuwa ne da masu sayar da abinci, ciki har da ‘yan mata masu sayar da kunu da awara. Ya kiyasta yawan mace-macen zuwa 117.

“Gaskiya ne, kasuwar Tumfa na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga. Ita ce sansaninsu. Duk wanda ya je can ya san ya shiga yankinsu,” in ji Musa.

Wani ɗan uwan wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce jirgin yaƙin sojoji ya fara shawagi a saman kasuwar domin bincike kafin ya dawo bayan wasu sa’o’i ya kai harin bam.

Ya kuma ce wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar kamar Fakai, Mayasa da Mashema na ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga saboda babu wata hukuma ta gwamnati a yankunan.

“Babu wata hukuma ta doka a ƙauyuka kamar Fakai, Mayasa da Mashema. ‘Yan bindiga ne suka zama alkalai da ‘yansanda,” in ji shi.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Ɗaliban Jami’ar Nasarawa da Aka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ɗaliban Jami’ar Nasarawa da Aka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.