Jam’iyyar APC ta soki tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, kan alƙawarin da ya yi na dawo da tallafin man fetur idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Atiku, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, ya yi wannan alƙawari ne yayin wani tattaunawa kai-tsaye da aka yi a shafinsa na Facebook.
Ya ce da farko bai yi adawa da cire tallafin man fetur ba, amma yanzu ya canja ra’ayinsa.
A cewarsa, har yanzu ba a bayyana yadda aka yi amfani da kuɗaɗen da aka aka samu bayan cire tallafin ba.
Atiku ya tambayi ko an yi amfani da kuɗaɗen wajen inganta harkokin lafiya, ilimi da tsaro.
Ya ce idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa a 2027, zai dawo da tallafin man fetur.
Ya kuma ce duk wanda ya sace kuɗaɗen tallafin zai dawo da su.
Sai dai Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar APC na ƙasa, Felix Morka, ya soki matakin na Atiku.
A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Morka ya ce Atiku ya sauya matsayinsa daga goyon bayan cire tallafin man fetur a 2023 zuwa alƙawarin dawo da shi a 2027.
Morka ya bayyana matakin na Atiku a matsayin alamar buƙatar samun goyon bayan jama’a.
Ya ce tsohon mataimakin shugaban ƙasar bai fahimci halin da tattalin arziƙin Nijeriya ke ciki ba kuma bai gabatar da wata ingantacciyar manufar tattalin arziƙi a matsayin madadin cire tallafin ba.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a lokacin rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu, 2023, a dandalin Eagle Square da ke Abuja.














