Sarkin Musulmi na Sakkwato, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya musanta wani rahoto da ke yawo a wasu kafofin sada zumunta da ke cewa ya buƙaci ƴan Nijeriya su goyi bayan sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa da Sashen Yaɗa Labarai na Sarkin Musulmi ya fitar ta hannun Prince Bashir Adefaka a ranar Talata, an buƙaci ƴan Nijeriya daga kowane ɓangare na al’umma da su yi watsi tare da yin Allah wadai da abin da ta bayyana a matsayin wani mugun ƙoƙari da ba na kishin ƙasa ba, na jawo martabar Sarkin Musulmi cikin siyasar jam’iyyu domin cimma muradun wasu.
Sanarwar ta ce: “ Cibiyoyin masarauta da addini da Sarkin Musulmi ke jagoranta cibiyoyi ne na uba ga kowa. Saboda haka, Mai Alfarma ba zai kauce daga wannan matsayi ba, inda yake bai wa ƴan siyasar Nijeriya shawara, albarkar sarauta da ta addini, da kuma jagoranci idan suka nemi hakan.
Ƙofofin Sarkin Musulmi a buɗe suke ga duk wanda ya zo wajensa, ba tare da la’akari da jam’iyyarsa ko ra’ayinsa na siyasa ba. A kodayaushe Mai Alfarma ya nuna cewa shi uba ne ga kowa, kuma zai ci gaba da mu’amala da dukkan ƴan Nijeriya ba tare da nuna bambanci ba.”
Saboda haka, Sashen Yaɗa Labaran ya yi kira ga jama’a da su ƙi duk wani yunƙuri na karkatar da matsayin Sarkin Musulmi ko danganta shi da yaƙin neman zaɓe ko takarar kowane mutum gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Sashen ya jaddada cewa Sarkin Musulmi, bisa matsayinsa na uba ga dukkan ƴan Nijeriya, zai ci gaba da jajircewa wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai, kwanciyar hankali da zaman tare cikin lumana tsakanin al’ummomi da mabiya addinai daban-daban a Nijeriya.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga ƴan jarida da masu amfani da kafofin sada zumunta da su kasance masu bin ƙa’idojin aikin jarida ta hanyar tantance sahihancin bayanai kafin yaɗa su, domin kauce wa ruɗar da jama’a ko jefa manyan cibiyoyin gargajiya da na addini cikin rikice-rikicen siyasa na jam’iyyu.














