ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Dattawan Kiristoci Sun Buƙaci Tinubu Kada Ya Tsaya Takara

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
Tinubu

Ƙungiyar Dattawan Kiristoci ta Ƙasa (NCEF) ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a shekarar 2027, tana mai danganta hakan da abin da ta bayyana a matsayin “raunin gwamnatinsa wajen magance matsalolin tsaro da tattalin arziki.”

A gefe guda kuma, Arewa Think Tank ta soki NCEF kan kiranta ga Shugaba Tinubu da ya janye daga shirin sake tsayawa takara, tana mai cewa babu wata ƙungiyar addini da ke da ikon yanke wa ƴan Nijeriya hukuncin wanda za su zaɓa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ƙarshen mako, wadda shugabanta, Dr. Samuel Danjuma Gani, ya sanya wa hannu, NCEF ta ce ana jagorantar ƙasar ne ta hanyar da ke haifar da ƙarin fargaba maimakon fata.

ADVERTISEMENT

A cewar ƙungiyar, maimakon Shugaba Tinubu ya nemi wa’adi na biyu, ya kamata ya mayar da sauran lokacin mulkinsa wajen sake fasalin Nijeriya da kuma samar da sabon Kundin Tsarin Mulki.

Dattawan sun ce gwamnatin mai ci ta gaza cika nauyin da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ɗora mata na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ƴan ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sun kuma soki tsarin Musulmi da Musulmi da aka yi a takarar shugaban ƙasa, suna mai bayyana shi a matsayin abin da bai dace ba, musamman a lokacin da ƴan ta’adda ke ci gaba da kai hare-hare a wasu sassan ƙasar, inda Kiristoci da dama suka kasance cikin waɗanda rikicin ya shafa.

Sanarwar ta ce: “Hanyar da gwamnatin Tinubu ke bi wajen jagorantar ƙasa tana ƙara haifar da fargaba maimakon fata. Wannan yanayi ya sa masu kishin ƙasa ba su da wani zaɓi face su roƙi Shugaba Tinubu da kada ya sake neman wa’adi na biyu. Maimakon haka, ya kamata ya yi amfani da sauran lokacin mulkinsa wajen sake fasalin Nijeriya da kuma samar mata da sabon Kundin Tsarin Mulki, domin ya bar kyakkyawan tarihi.”

Dattawan Kiristocin sun kuma yi kira ga ƙabilu daban-daban, ƙungiyoyin al’adu da sauran ƙungiyoyin masu ruwa da tsaki da su fara shirye-shiryen tabbatar da amincewa da sabon Kundin Tsarin Mulki kafin babban zaɓen shekarar 2027.

Sun yi gargaɗin cewa kada a ɗauki haƙurin ƴan Nijeriya da wasa, suna mai cewa al’umma na matuƙar ɗokin ganin canji.

Tinubu
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

2027: Sabuwar Muhawara Ta Kaure Kan Cancantar Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.