Fitar da sunan Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2027 da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta yi, ya sake tada da zazzafar muhawara kan cece-kuce game da takardun karatunsa, wanda ya fara fitowa tun a zaɓen 2023.
Wannan dai kamar yadda INEC ta bayyana cewa ba ta bincikar sahihancin takardun karatu da sauran shaidar da ƴan takara suka gabatar kafin a fitar da sanyasu.
A cikin takardun cancantar ƴan takarar shugabancin da INEC ta fitar a ranar Asabar, INEC ta saka cewa Tinubu ya samu shaidar digiri a fannin kimiyyar kasuwanci daga jami’ar Chicago da ke ƙasar Amurka a shekarar 1979, ba tare da wani takardar shaidar makarantar firamare ko sakandare a cikin takardun da aka bayyana ba.
Wuraren da aka tanada don saka shaidar karatun firamare da sakandare ba a cika su ba. Akwai an saka takardar digiri na shugaban da takardar shaidar kammala bautar ƙasa (NYSC) a matsayin takardunsa.
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya lissafa ƙwarewarsa ta shadai karatun firamare da ya samu a 1954 da na sakandare da ya samu a 1961 ba tare da ambaton sunayen makarantu ba. Haka nan ya nuna cewa ya samu digiri na biyu a 2020 daga jami’ar Anglia Ruskin.
Shi kuwa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya nuna cewa ya halarci makarantar firamare ta St. Augustine, Anambra (1973) da makarantar sakandare ta Christ the King College a 1978 da kuma jami’ar Nijeriya ta Nsukka, inda ya samu digiri a fannin falsafa a 1984.
Rashin ambaton takardun makarantar firamare da sakandare na Tinubu ya dawo da tunanin gwagwarmayar shari’a da ta biyo bayan zaɓen shugaban ƙasa na 2023, lokacin da Atiku, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP ya zargi cewa ya miƙa takardun bogi ga INEC.
A wancen lokaci, duk da cewa jami’ar Amurka ta tabbatar cewa Tinubu ya kammala karatunsa daga wannan makaranta a shekarar 1979, rikice-rikice kan takardar shaidar digiri da ake zargin an miƙa wa INEC sun zama ɗaya daga cikin manyan batutuwa a shari’ar bayan zaɓen. Kotun sauraron ƙarar zaɓen shugaban ƙasa da kotun ƙoli sun yi watsi da ƙarar tare da tabbatar da zaɓen Tinubu.
A cikin tambayoyi daban-daban da aka yi, lauyoyi da jam’iyyun adawa sun tambayi dalilin da ya sa ba a saka takardun shaidar makarantar firamare da sakandare na shugaban ƙasa a cikin takardun da hukumar zaɓe ta fitar ba.
Sun ce rashin saka takardun ya sake sanya damuwar jama’a da ba a warware ba game da cancantar karatun Tinubu, suna kiran a yi ƙarin gaskiya wajen bayyana takardun ƴan takara.
Wani babban lauya a Nijeriya, Mumini Jimoh, ya ce karatun makaranta har zuwa matakin sakandare na daga cikin manyan sharuɗɗan da ake buƙata ga ƴan takarar shugaban ƙasa, wanda hakan ke sa kusan ba zai yuwu ba ga wanda bai samu wannan takardu ba.
Shi ma wani babban lauya, Mohammed Abeni, ya ce rashin ambaton shaidar makarantar sakandare daga cikin takardun da aka ɗora yana haifar da tambayoyi da kuma shakku, musamman ma a ciki halin da ake ciki na cece-kuce da suka biyo baya kan bayyanan ilimin shugaban ƙasa.
Ƙwararren lauya, Danjuma John, ya ce idan mutum ya cancanci tsayawa takarar shugaban ƙasa a Nijeriya ƙarƙashin dokokin mulki na yanzu, dole ne ɗan takara ya cika wasu muhimman sharuɗɗa, ya kasance yana da aƙalla takardar shaidar makarantarsa.
Duk da haka, Lauya Taiye Oniyide bai yarda ba, yana jaddada cewa rashin ambaton ba ya haifar da wata illa ta doka ta tanada, sannan kuma bai kamata a cakuɗa shi da cancantar da kundin tsarin mulki ya tanada ba.
INEC ta bayyana cewa ƙarƙashin dokar zaɓe ta 2026, aikinta shi ne ta wallafa bayanan ƴan takara da takardunsu don jama’a su duba, yayin da duk wata ƙalubale kan gaskiya ko ingancin waɗannan takardun, kotu ce za ta iya warwarewa.
Mataimakin daraktan yaɗa labarai na INEC, Wilfred Osilama Ifogah, ya bayyana haka a yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai kan wallafa bayanan cancantar ƴan takara na zaɓen 2027.
Jam’iyyar ADC ta zargi Tinubu da ƙoƙarin ɓoye wani abu ta hanyar ƙin saka takardun shaidar makarantar firamare da sakandare a shafin INEC.
Sakatare yaɗa labarai na jam’iyyar, Malam Bolaji Abdullahi, ya shaida cewa, “Ta hanyar barin waɗannan matakan ilimi, kamar yana ba da gaskiya ga jita-jitar cewa Tinubu yana da wani abu da yake ɓoyewa game da da’awarsa. A gare mu a matsayin jam’iyya, shugaban Nijeriya bai kamata ya kasance da irin wannan ɓoyayyiyar magana a kansa ba.
Haka kuma, sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar NDC, Osa Director, ya bayyana cewa rashin saka takardun shaida na makarantar firamare da sakandare na Tinubu a cikin shafin INEC a matsayin abin mamaki.
Ya ce, “Abin mamaki ne saboda duk mun san cewa ba za ka iya samun takardar shaidar jami’a ba tare da takardun makarantar firamare da sakandare ba, waɗanda suke a matsayin sharaɗi.”
Duk da ƙoƙarin jin martani daga fadar shugaban ƙasa ya ci tura, domin ba a samu wayar mai bai wa shagaban ƙasa shawara ta musamman kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, yayin da shi ma mai ba shagaban ƙasa shawara kan harkokin sadarwar, Daniel Bwala, bai amsa kiran wayarsa ba.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, saƙonni da aka aika wasu ta WhatsApp mataimakan shugaban ƙasan guda biyu ba su amsa ba.














