Ibrahim Sani Shawai shi ne mai magana da yawun Sardaunan Gombe, Dr Jamil isyaku Gwamna ɗaya daga cikin waɗanda ke neman takarar kujerar gwamnan Jihar Gombe a jam’iyyar APC. A tattaunawarsa da Editanmu Bello Hamza, ya yi bayani a kan ƙwarewarsa da kuma irin tanadin ayyukan alhairi da ya shirya yi wa al’ummar jihar Gombe in ya kai ga ci. Ga dai yadda hirar ta kasance;.
Da farko, ko zaka ba mu bayani a taƙaice a kan wane ne Dr. Jamil Isyaku Gwamna
Dr jamilu Isyaku Gwamna, wanda aka fi sani da Sardaunan Gombe, an haife shi ne a ƙaramar Hukumar Gombe da ke Jihar Gombe. Ya yi firamare da sakandare dukka a Gombe. Daga nan ya tafi Jami’ar ABU Zaria, inda ya yi digirinsa na farko a fannin Tattalin Arziki, wato Accountancy, a shekara ta 1986. Daga nan ya tafi Jami’ar Metropolitan da ke birnin Landan inda ya kammala digirinsa na biyu a shekara ta 2004 a harkokin tattalin azriƙi da hada-hadar kuɗaɗe, wato “Economics and Finance”. Haka kuma ya ci gaba da digirinsa na uku a fannin tattalin Arziƙi a dai wannan Jami’ar da ke birnin Landan, inda ya kammala a shekara ta 2008.
Dr. Jamil ya yi aiki a wurare daban-daban, kama daga gwamnati da kuma kamfanoni. Ya kuma yi tafiye-tafiye zuwa kasashe daban-daban a Duniya.
- Gidauniyar Bukola Saraki Za Ta Fara Raba Abincin Buɗe Baki Daga Gobe
- Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
A halin yanzu guguwar siyasar 2027 ta kaɗa, wa kake ganin ya dace ya jagoranci jihar Gombe a matsayin Gwamna a wannan lokacin?
Da farko dai, dole ne mu fara da yaba wa irin gagarumar nasarar da Jihar Gombe ta samu a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya. Babu shakka, an samu sauyi a fannoni da dama; daga inganta ababen more rayuwa, zuwa bunƙasa tattalin arziki da kuma ƙoƙarin daidaita harkokin gwamnati cikin tsari mai kyau. Gwamna ya bunƙasa harkokin noma, ya samar da kayayyakin inganta karatu daga mataki na firamare har zuwa gaba da sakandare.
A irin wannan yanayi, abin da Gombe ke buƙata a yanzu shi ne shugaba wanda zai gina a kan wannan turba, ba wanda zai rushe ta ba. Mutumin da zai zo da sabon hangen nesa amma kuma yana mutunta nasarorin da aka riga aka samu.
A ganina, lokaci ya yi da za a zaɓi shugaba mai kishin jama’a, mai gaskiya da riƙon amana, wanda zai iya ɗaukar Gombe daga matakin da take kai yanzu zuwa wani sabon matsayi mafi girma.
Wani sabon salon mulki kake ganin Dr. Jamil Isiyaku Gwamna (Sardaunan Gombe) zai bijiro da shi a Jihar Gombe da ba a saba gani ba?
Idan muka kalli irin tubalin da Gwamnatin Muhammadu Inuwa Yahaya ta shimfiɗa, za mu ga cewa akwai kyakkyawan tushe da duk wani shugaba mai hangen nesa zai iya gini a kai.
Dr. Jamil Isiyaku Gwamna (Sardaunan Gombe) mutum ne mai fahimta da hangen nesa. Salon mulkinsa zai zo ne da sabbin dabaru da suka haɗa da: Inganta amfani da fasaha wajen tafiyar da gwamnati, Samar da ƙarin damammaki ga matasa Maza da Mata, Ƙara buɗe ƙofa domin zuba jari da bunƙasa kasuwanci da kuma ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnati da al’umma.
Abin da zai bambanta shi shi ne yadda zai haɗa sabbin tunani da kuma ci gaba da kyawawan manufofin da gwamnatin Inuwa Yahaya ta fara, domin a samu ci gaba mai ɗorewa.
Ganin mutane da dama sun nuna sha’awarsu na zama Gwamnan Gombe a wannan lokacin, ya kake ganin tagomashinsa?
Haƙiƙa, yawan masu neman kujera alama ce ta dimokuraɗiyya mai ƙarfi, kuma hakan ma wata nasara ce da za a danganta da kyakkyawan yanayin siyasa da gwamnatin Muhammadu Inuwa Yahaya ta samar.
Amma duk da haka, ba yawan masu nema ne ke ba da nasara ba, inganci da karɓuwa ne suka fi tasiri.
Game da Sardaunan Gombe, yana da wasu muhimman abubuwa da ke ƙara masa armashi: sun kuma haɗa da, Karɓuwa a tsakanin jama’a musamman matasa, Tarihi mai kyau da mutunci da kuma mutuntawa, Fahimtar tsarin gwamnati da kuma yadda za a gina kan nasarorin da aka samu da kuma salon siyasa mai tsafta da mutunta kowa da kuma ba kowa haƙƙinsa.
Wadannan su ne ginshiƙan da ke sa a duba shi a matsayin wanda ya tsere sa a.
A baya Dr. Jamilu Gwamna ya taka wani matsayi na ɗaukaka a rayuwarsa, waɗanne abubuwa ya yi wa al’ummar Jihar Gombe da zai zama hujja a gare su na zaɓensa?
Abubuwan alkhairin da ya yi wa al’ummar Jihar Gombe ba za su ƙididdigu ba, amma ga wasu daga ciki;
Samarwa matasan Gombe aiki a hukumar KEDCO da Kaduna Electric Sama da Mutum dubu ɗaya, Samarwa mutane daban-daban aiki a Gombe Water Board sama da Mutum dubu ɗaya, Lokacin yana shugabantar hukumar. Haka kuma ya bayar da gidaje da filaye kyauta domin ci gaban ilimi a Jihar Gombe, ya kuma raba motoci ga ƙungiyoyin addini domin sauƙaƙa musu zirga-zirgar ayyukansu, ya kuma gyara masallatai wato ‘renoɓation’ da kuma gina wasu masallatan sabbi.
Ya kuma raba wa mutane abun hawa, kama daga motoci da baburan hawa domin inganta rayuwarsu. Ya tallafa wajen aurar da ‘yaƴan marasa ƙarfi da yawa tare da yi musu kayan ɗaki. A fannin lafiya na san yaron da maciji ya sara a Kaltungo daga ƙarshe cancer ta shiga ƙafar aka yanke, Sardauna ya kai shi wani asibiti a Inugu aka yi masa ƙafa na musamman. Haka kuma akwai waɗanda aka yi wa tiyata da ya ɗauki nauyin su da yawa.
Haka kuma a ƙarƙashin Gidauniyar Agaji ta ‘Sardauna Foundation’ an raba wa mata keken ɗinki, da injin markaɗe, da firinjin ƙanƙara, da kuma bayar da jari domin dogora da kai. Ya biya wa yara ƴan Gombe su 39 kuɗin makaranta a Yamusa science Academy Birnin Kebbi, kuma dukkanin su sun kammala. Da dai ayyukan alhairi na bunƙasa rayuwar al’umma.
Abin da ya fi ban mamaki game da halayyarsa shi ne jajircewarsa wajen haɗakan al’umma da magance damuwarsu. Shi mai fafutukar ƙarfafa mata ne, mai ba da shawara ga matasa, kuma mai fafutukar kare haƙƙin naƙasassu. Ɗabi’arsa ta son zaman lafiya ta sa ya sami girmamawa daga ƴan jihar Gombe waɗanda ke godiya da halayyarsa ta yin shawara da haɗɗaka fahimtar juna, ba tare da nuna banbancin addini ko ƙabila ko kuma al’ada ba.
Idan Allah Ya sa Dr. Jamilu Gwamna ya zama Gwamnan Jihar Gombe, waɗanne fannoni kake ganin zai fi bai wa fifiko a mulkinsa?
Dr. Jamilu Gwamna zai fi ba da fifiko a fannin gina al’umma da kuma fannin ilimi. Yana da fahimtar cewa waɗannan su ne ginshiƙan da ake samar da al’umma mai nagarta. A wajensa, gina al’umma ta hanyar samar musu da ayyukan yi, da koya musu sana’o’i, da ba su jari don su zamo masu dogaro da kansu, shi ne kan gaba, kafin a yi batun samar da abubuwan more rayuwa.
Ta fuskar ilimi kuwa, a wajen sa, ilimi shi ne ginshikin cigaban kowacce al’umma. Ya yi imanin cewa kowane yaro da yarinya ƴan Jihar Gombe sun cancanci samun ingantaccen ilimi, ba tare da la’akari da asalinsu ko yanayin arziƙinsu ba. Yana da burin inganta horar da malamai, da inganta yanayin koyo da koyarwa, da kuma samar da tallafin karatu ga ɗaliban da ba su da galihu, tare da tabbatar da cewa matasanmu suna da ƙwarewa da ilimin da suke buƙata don samun nasara a rayuwarsu.
Ko akwai wani kira na musamman da zaka yi wa al’ummar Jihar Gombe?
Ina kira ga al’ummar Jihar Gombe da su ci gaba da goyon bayan manufofi da shirye-shiryen ci gaba irin waɗanda gwamnatin Muhammadu Inuwa Yahaya ta kawo. Hakazalika: Su zaɓi shugabanni bisa cancanta da nagarta. Su guji siyasar rarrabuwar kai da ƙiyayya. Su ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya. Su ba da dama ga matasa domin su taka rawa a ci gaban Jihar Gombe.
Idan muka haɗa kai, muka gina a kan nasarorin da aka riga aka samu, babu shakka Gombe za ta zama abin koyi a Nijeriya.
Gombe na kan tafarkin ci gaba. Abin da ya rage shi ne a tabbatar an samu shugabanci mai ɗorewa wanda zai ci gaba daga inda aka tsaya, ba tare da katse wannan kyakkyawan tafiya ba.
Mun
gode ƙwarai da gaske
Nima na gode















Discussion about this post