Gwamnatin Jihar Bauchi ta umarci dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da ke da niyyar tsayawa takara a zaɓukan fidda gwani na jam’iyyunsu da su yi murabus daga mukamansu kafin ko zuwa a ranar Juma’a, 24 ga Afrilu, 2026.
Wannan umarni na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar a ranar Laraba.Sanarwar ta bayyana cewa umarnin ya zo ne domin bin tanade-tanaden Dokar Zaɓe ta 2026 (da aka yi wa kwaskwarima).
- Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
- Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
- Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa
- Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
- Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza
A cewar sanarwar, matakin ya yi daidai da ƙa’idojin doka da ke tsara yadda masu riƙe da muƙaman gwamnati za su shiga harkokin zaɓe, tare da tabbatar da cikakken bin doka.
Gwamnatin ta kuma nuna godiya ga waɗanda abin ya shafa bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban Jihar Bauchi, tare da yi musu fatan alheri a rayuwarsu na gaba.
A cewar sanarwar, an kuma umarci dukkan waɗanda za su ajiye aikin nasu da su miƙa dukkan ragama ofisoshinsu da ƙadarorin gwamnati da ke hannunsu, ga jami’in ya dace a cikin ma’aikatunsu, sassa da hukumominsu (MDAs).














