Gwamnatin Jihar Bauchi ta umarci dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da ke da niyyar tsayawa takara a zaɓukan fidda gwani na jam’iyyunsu da su yi murabus daga mukamansu kafin ko zuwa a ranar Juma’a, 24 ga Afrilu, 2026.
Wannan umarni na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar a ranar Laraba.Sanarwar ta bayyana cewa umarnin ya zo ne domin bin tanade-tanaden Dokar Zaɓe ta 2026 (da aka yi wa kwaskwarima).
- Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
- An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
- Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
- Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
- Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
A cewar sanarwar, matakin ya yi daidai da ƙa’idojin doka da ke tsara yadda masu riƙe da muƙaman gwamnati za su shiga harkokin zaɓe, tare da tabbatar da cikakken bin doka.
Gwamnatin ta kuma nuna godiya ga waɗanda abin ya shafa bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban Jihar Bauchi, tare da yi musu fatan alheri a rayuwarsu na gaba.
A cewar sanarwar, an kuma umarci dukkan waɗanda za su ajiye aikin nasu da su miƙa dukkan ragama ofisoshinsu da ƙadarorin gwamnati da ke hannunsu, ga jami’in ya dace a cikin ma’aikatunsu, sassa da hukumominsu (MDAs).














