Hukumar Kwallon Kafa ta Firimiya ta Nijeriya (NPFL) ta ci tarar ƙungiyar Kano Pillars Naira miliyan 15 bayan karya dokokin gasar da aka samu a wasan da suka buga da Rivers United ranar Lahadi, 19 ga Afrilu, 2026. A cikin wata sanarwa mai tsauri, hukumar ta zargi ƙungiyar da gaza samar da isasshen tsaro a filin wasan, lamarin da ya bai wa wasu damar shiga wuraren da ba a amince ba.
Lamarin ya ƙara tsananta ne bayan da magoya baya suka kutsa cikin fili, wanda ya jefa ‘yan wasa da alƙalai cikin haɗari. NPFL ta bayyana halin da magoya bayan suka nuna a matsayin abin da zai ɓata martabar gasar, tare da zargin an yi barazana da cin zarafi ga alƙalan wasa.
- Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
- ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
- Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
- Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
- Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
A cikin bayanin hukuncin, an ci Kano Pillars tarar Naira miliyan 4 kan rashin tsaro, da miliyan 3 kan rashin kyawawan ɗabi’ar ƴan kallo, da kuma wata miliyan 3 saboda gazawa wajen daƙile magoya baya da suka ci zarafin alƙalai. Haka kuma an ƙara musu miliyan 3 kan rashin ɗa’a ga alƙalai da miliyan 2 kan haddasa tsaiko da janyo dakatar da wasa na wani lokaci.
Baya ga tarar kuɗi, an umurci Kano Pillars da buga wasanninsu uku na gida ba tare da ƴan kallo ba, ciki har da wasansu na ƙarshe a wannan kakar da kuma wasu biyu a kakar mai zuwa.
Hukumar NPFL ta jaddada cewa ba za ta lamunci irin wannan rikici daga magoya baya ba, tare da bai wa ƙungiyar wa’adin awanni 48 domin ɗaukaka ƙara kan hukuncin.














