Hukumar Kwallon Kafa ta Firimiya ta Nijeriya (NPFL) ta ci tarar ƙungiyar Kano Pillars Naira miliyan 15 bayan karya dokokin gasar da aka samu a wasan da suka buga da Rivers United ranar Lahadi, 19 ga Afrilu, 2026. A cikin wata sanarwa mai tsauri, hukumar ta zargi ƙungiyar da gaza samar da isasshen tsaro a filin wasan, lamarin da ya bai wa wasu damar shiga wuraren da ba a amince ba.
Lamarin ya ƙara tsananta ne bayan da magoya baya suka kutsa cikin fili, wanda ya jefa ‘yan wasa da alƙalai cikin haɗari. NPFL ta bayyana halin da magoya bayan suka nuna a matsayin abin da zai ɓata martabar gasar, tare da zargin an yi barazana da cin zarafi ga alƙalan wasa.
- ‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
- ‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano
- Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
- Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
- An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
A cikin bayanin hukuncin, an ci Kano Pillars tarar Naira miliyan 4 kan rashin tsaro, da miliyan 3 kan rashin kyawawan ɗabi’ar ƴan kallo, da kuma wata miliyan 3 saboda gazawa wajen daƙile magoya baya da suka ci zarafin alƙalai. Haka kuma an ƙara musu miliyan 3 kan rashin ɗa’a ga alƙalai da miliyan 2 kan haddasa tsaiko da janyo dakatar da wasa na wani lokaci.
Baya ga tarar kuɗi, an umurci Kano Pillars da buga wasanninsu uku na gida ba tare da ƴan kallo ba, ciki har da wasansu na ƙarshe a wannan kakar da kuma wasu biyu a kakar mai zuwa.
Hukumar NPFL ta jaddada cewa ba za ta lamunci irin wannan rikici daga magoya baya ba, tare da bai wa ƙungiyar wa’adin awanni 48 domin ɗaukaka ƙara kan hukuncin.













