ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Jam’iyyun Adawa Na Ci Gaba Da Fama Da Shari’o’i A Gaban Kotuna

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
Kotu

Rahotanni na bayyana cewa yawan shari’o’i da ke karuwa da suka shafi jam’iyyun adawa a Nijeriya na jefa shakku kan damar su gabanin zaben 2027, yayin da shirye-shiryen siyasa suka fara kakama kafin yadda ake tsammani da kuma yadda doka ta tanada.

Wadannan rikice-rikicen sun kara zurfafa rabuwar kan a cikin jam’iyyun adawa, sannan suna barazana ga hadin kan jam’iyya da kuma tsarin dimokuradiyya baki daya.

  • Tawagar Atiku Ta Isa Bauchi Don Halartar Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

Jam’iyyar PDP ta kasace babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya tun daga 2015, ita ce wadda abin ya fi shafa. Jerin hukunci daga kotu da ke karo da juna ya kai ga hargitsi a babban ofishin jam’iyyar a ranar Talata, wanda lamarin ya haifar da ‘ya kallo da dama tare da saka alamar tamaya ko jam’iyyar za ta ci gaba da dorewa iko kuma za ta mutu.

ADVERTISEMENT

Yayin da wasu masana suke ba da shawara cewa PDP na kan hanyar samun kwanciyar hankali bayan babban taronta na kasa, wanda aka gudanar duk da umarnin kotu biyu da suka dakatar da shi, har yanzu akwai sauran rina a kaba, inda bangaren ministan Abuja, Nyesom Wike ke jagoranta ya yi watsi da taron sakamon korar sa da aka yi, wanda hakan na iya neman daukar matakin shari’a.

An sami manyan shari’u guda uku game da taron PDP, guda biyu a babban kotun tarayya a Abuja da guda daya a babban kotun Jihar Oyo a Ibadan. A Abuja, reshen da ke adawa da taron, wanda ya kunshi mabiyan Wike da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, sun sami hukuncin dakatar da taron, inda daya ya bayyana cewa an hana Lamido saya fom din takarar shugaban jam’iyyar na kasa.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

A babban kotun Jihar Oyo, a cikin karar da magoya bayan gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde suka shigar, ta amince da taron, duk da cewa har yanzu ba a yanke hukunci a mahangar shari’a ba. Bangaren Makinde da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammed sun goyi bayan Kabiru Tanimu Turaki (SAN) a matsayin sabon shugaban jam’iyyar tare da goyon bayan kwamitin amintattu karkashin tsohon shugaban majalisar dattawa, Adolphus Wabara.

Kazalika, jam’iyyar LP, wadda ta zo ta uku a zaben shugaban kasa na 2023, ta shiga rikicin shugabanci mai tsawo. Bangarori masu hamayya sun yi amfani da hukuncin kotu daban-daban don tabbatar da sahihancinsu, har ma suna kin bin hukuncin kotun koli wajen warware rigingimun. Masana na gargadi cewa wannan ci gaba da rikici na iya raunana damar jam’iyyar wajen shirya zaben fid da gwani da kuma fitar da ‘yan takara masu inganci a shekarar 2027.

Ita ma sabuwar jam’iyyar NNPP, wadda ta zo ta hudu a 2023, na fuskantar irin wannan rikici. Hukuce-hukuci kotuna da dama sun amince da rassan daban-daban, wanda ya sa ayyukan jam’iyyar sun tsaya cak.

Jam’iyyar ADC, wadda yanzu ke karkashin jagorancin hadin gwiwar ‘yan adawa, tana fama da rikice-rikicen shari’a na cikin gida. Tsohon dan takarar shugaban kasa, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci hadi gwiwar jam’iyyar a gaba kotu, inda har yanzu ba yanke hukunci ba, abin da ke nuna irin mawuyaci hali da jam’iyyar za ta iya fadawa kafin 2027.

A farkon wannan shekara ce, kotun koli ta yanke hukunci da nufin warware rikice-rikice na cikin gida a cikin PDP da LP, amma lamarin ya ci tura. Kotun kolin ta jaddada cewa al’amuran cikin gida na jam’iyya, ciki har da neman takarar shugabanci, galibi suna karkashin kundin tsarin jam’iyya kuma ba sa karkashin hukuncin kotu, sai in har an take hakkokin Dan’adam. Duk da haka, hukunce-hukunce masu karo da juna na kananan kotuna sun raunana wannan ka’ida, inda masana shari’a suka danganta hakan ga juya hukunci a kotuna.

Kotu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
Kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.