ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Jam’iyyun Adawa Na Ci Gaba Da Fama Da Shari’o’i A Gaban Kotuna

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
Kotu

Rahotanni na bayyana cewa yawan shari’o’i da ke karuwa da suka shafi jam’iyyun adawa a Nijeriya na jefa shakku kan damar su gabanin zaben 2027, yayin da shirye-shiryen siyasa suka fara kakama kafin yadda ake tsammani da kuma yadda doka ta tanada.

Wadannan rikice-rikicen sun kara zurfafa rabuwar kan a cikin jam’iyyun adawa, sannan suna barazana ga hadin kan jam’iyya da kuma tsarin dimokuradiyya baki daya.

  • Tawagar Atiku Ta Isa Bauchi Don Halartar Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

Jam’iyyar PDP ta kasace babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya tun daga 2015, ita ce wadda abin ya fi shafa. Jerin hukunci daga kotu da ke karo da juna ya kai ga hargitsi a babban ofishin jam’iyyar a ranar Talata, wanda lamarin ya haifar da ‘ya kallo da dama tare da saka alamar tamaya ko jam’iyyar za ta ci gaba da dorewa iko kuma za ta mutu.

ADVERTISEMENT

Yayin da wasu masana suke ba da shawara cewa PDP na kan hanyar samun kwanciyar hankali bayan babban taronta na kasa, wanda aka gudanar duk da umarnin kotu biyu da suka dakatar da shi, har yanzu akwai sauran rina a kaba, inda bangaren ministan Abuja, Nyesom Wike ke jagoranta ya yi watsi da taron sakamon korar sa da aka yi, wanda hakan na iya neman daukar matakin shari’a.

An sami manyan shari’u guda uku game da taron PDP, guda biyu a babban kotun tarayya a Abuja da guda daya a babban kotun Jihar Oyo a Ibadan. A Abuja, reshen da ke adawa da taron, wanda ya kunshi mabiyan Wike da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, sun sami hukuncin dakatar da taron, inda daya ya bayyana cewa an hana Lamido saya fom din takarar shugaban jam’iyyar na kasa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

A babban kotun Jihar Oyo, a cikin karar da magoya bayan gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde suka shigar, ta amince da taron, duk da cewa har yanzu ba a yanke hukunci a mahangar shari’a ba. Bangaren Makinde da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammed sun goyi bayan Kabiru Tanimu Turaki (SAN) a matsayin sabon shugaban jam’iyyar tare da goyon bayan kwamitin amintattu karkashin tsohon shugaban majalisar dattawa, Adolphus Wabara.

Kazalika, jam’iyyar LP, wadda ta zo ta uku a zaben shugaban kasa na 2023, ta shiga rikicin shugabanci mai tsawo. Bangarori masu hamayya sun yi amfani da hukuncin kotu daban-daban don tabbatar da sahihancinsu, har ma suna kin bin hukuncin kotun koli wajen warware rigingimun. Masana na gargadi cewa wannan ci gaba da rikici na iya raunana damar jam’iyyar wajen shirya zaben fid da gwani da kuma fitar da ‘yan takara masu inganci a shekarar 2027.

Ita ma sabuwar jam’iyyar NNPP, wadda ta zo ta hudu a 2023, na fuskantar irin wannan rikici. Hukuce-hukuci kotuna da dama sun amince da rassan daban-daban, wanda ya sa ayyukan jam’iyyar sun tsaya cak.

Jam’iyyar ADC, wadda yanzu ke karkashin jagorancin hadin gwiwar ‘yan adawa, tana fama da rikice-rikicen shari’a na cikin gida. Tsohon dan takarar shugaban kasa, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci hadi gwiwar jam’iyyar a gaba kotu, inda har yanzu ba yanke hukunci ba, abin da ke nuna irin mawuyaci hali da jam’iyyar za ta iya fadawa kafin 2027.

A farkon wannan shekara ce, kotun koli ta yanke hukunci da nufin warware rikice-rikice na cikin gida a cikin PDP da LP, amma lamarin ya ci tura. Kotun kolin ta jaddada cewa al’amuran cikin gida na jam’iyya, ciki har da neman takarar shugabanci, galibi suna karkashin kundin tsarin jam’iyya kuma ba sa karkashin hukuncin kotu, sai in har an take hakkokin Dan’adam. Duk da haka, hukunce-hukunce masu karo da juna na kananan kotuna sun raunana wannan ka’ida, inda masana shari’a suka danganta hakan ga juya hukunci a kotuna.

Kotu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.