ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Jam’iyyun Adawa Na Ci Gaba Da Fama Da Shari’o’i A Gaban Kotuna

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
Kotu

Rahotanni na bayyana cewa yawan shari’o’i da ke karuwa da suka shafi jam’iyyun adawa a Nijeriya na jefa shakku kan damar su gabanin zaben 2027, yayin da shirye-shiryen siyasa suka fara kakama kafin yadda ake tsammani da kuma yadda doka ta tanada.

Wadannan rikice-rikicen sun kara zurfafa rabuwar kan a cikin jam’iyyun adawa, sannan suna barazana ga hadin kan jam’iyya da kuma tsarin dimokuradiyya baki daya.

  • Tawagar Atiku Ta Isa Bauchi Don Halartar Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

Jam’iyyar PDP ta kasace babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya tun daga 2015, ita ce wadda abin ya fi shafa. Jerin hukunci daga kotu da ke karo da juna ya kai ga hargitsi a babban ofishin jam’iyyar a ranar Talata, wanda lamarin ya haifar da ‘ya kallo da dama tare da saka alamar tamaya ko jam’iyyar za ta ci gaba da dorewa iko kuma za ta mutu.

ADVERTISEMENT

Yayin da wasu masana suke ba da shawara cewa PDP na kan hanyar samun kwanciyar hankali bayan babban taronta na kasa, wanda aka gudanar duk da umarnin kotu biyu da suka dakatar da shi, har yanzu akwai sauran rina a kaba, inda bangaren ministan Abuja, Nyesom Wike ke jagoranta ya yi watsi da taron sakamon korar sa da aka yi, wanda hakan na iya neman daukar matakin shari’a.

An sami manyan shari’u guda uku game da taron PDP, guda biyu a babban kotun tarayya a Abuja da guda daya a babban kotun Jihar Oyo a Ibadan. A Abuja, reshen da ke adawa da taron, wanda ya kunshi mabiyan Wike da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, sun sami hukuncin dakatar da taron, inda daya ya bayyana cewa an hana Lamido saya fom din takarar shugaban jam’iyyar na kasa.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

A babban kotun Jihar Oyo, a cikin karar da magoya bayan gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde suka shigar, ta amince da taron, duk da cewa har yanzu ba a yanke hukunci a mahangar shari’a ba. Bangaren Makinde da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammed sun goyi bayan Kabiru Tanimu Turaki (SAN) a matsayin sabon shugaban jam’iyyar tare da goyon bayan kwamitin amintattu karkashin tsohon shugaban majalisar dattawa, Adolphus Wabara.

Kazalika, jam’iyyar LP, wadda ta zo ta uku a zaben shugaban kasa na 2023, ta shiga rikicin shugabanci mai tsawo. Bangarori masu hamayya sun yi amfani da hukuncin kotu daban-daban don tabbatar da sahihancinsu, har ma suna kin bin hukuncin kotun koli wajen warware rigingimun. Masana na gargadi cewa wannan ci gaba da rikici na iya raunana damar jam’iyyar wajen shirya zaben fid da gwani da kuma fitar da ‘yan takara masu inganci a shekarar 2027.

Ita ma sabuwar jam’iyyar NNPP, wadda ta zo ta hudu a 2023, na fuskantar irin wannan rikici. Hukuce-hukuci kotuna da dama sun amince da rassan daban-daban, wanda ya sa ayyukan jam’iyyar sun tsaya cak.

Jam’iyyar ADC, wadda yanzu ke karkashin jagorancin hadin gwiwar ‘yan adawa, tana fama da rikice-rikicen shari’a na cikin gida. Tsohon dan takarar shugaban kasa, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci hadi gwiwar jam’iyyar a gaba kotu, inda har yanzu ba yanke hukunci ba, abin da ke nuna irin mawuyaci hali da jam’iyyar za ta iya fadawa kafin 2027.

A farkon wannan shekara ce, kotun koli ta yanke hukunci da nufin warware rikice-rikice na cikin gida a cikin PDP da LP, amma lamarin ya ci tura. Kotun kolin ta jaddada cewa al’amuran cikin gida na jam’iyya, ciki har da neman takarar shugabanci, galibi suna karkashin kundin tsarin jam’iyya kuma ba sa karkashin hukuncin kotu, sai in har an take hakkokin Dan’adam. Duk da haka, hukunce-hukunce masu karo da juna na kananan kotuna sun raunana wannan ka’ida, inda masana shari’a suka danganta hakan ga juya hukunci a kotuna.

Kotu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.