ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Jam’iyyun Adawa Na Ci Gaba Da Fama Da Shari’o’i A Gaban Kotuna

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
6 months ago
Kotu

Rahotanni na bayyana cewa yawan shari’o’i da ke karuwa da suka shafi jam’iyyun adawa a Nijeriya na jefa shakku kan damar su gabanin zaben 2027, yayin da shirye-shiryen siyasa suka fara kakama kafin yadda ake tsammani da kuma yadda doka ta tanada.

Wadannan rikice-rikicen sun kara zurfafa rabuwar kan a cikin jam’iyyun adawa, sannan suna barazana ga hadin kan jam’iyya da kuma tsarin dimokuradiyya baki daya.

  • Tawagar Atiku Ta Isa Bauchi Don Halartar Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Sin Ta Ciri Tuta A Jagorancin Ayyukan Dakile Sauyin Yanayi 

Jam’iyyar PDP ta kasace babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya tun daga 2015, ita ce wadda abin ya fi shafa. Jerin hukunci daga kotu da ke karo da juna ya kai ga hargitsi a babban ofishin jam’iyyar a ranar Talata, wanda lamarin ya haifar da ‘ya kallo da dama tare da saka alamar tamaya ko jam’iyyar za ta ci gaba da dorewa iko kuma za ta mutu.

ADVERTISEMENT

Yayin da wasu masana suke ba da shawara cewa PDP na kan hanyar samun kwanciyar hankali bayan babban taronta na kasa, wanda aka gudanar duk da umarnin kotu biyu da suka dakatar da shi, har yanzu akwai sauran rina a kaba, inda bangaren ministan Abuja, Nyesom Wike ke jagoranta ya yi watsi da taron sakamon korar sa da aka yi, wanda hakan na iya neman daukar matakin shari’a.

An sami manyan shari’u guda uku game da taron PDP, guda biyu a babban kotun tarayya a Abuja da guda daya a babban kotun Jihar Oyo a Ibadan. A Abuja, reshen da ke adawa da taron, wanda ya kunshi mabiyan Wike da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, sun sami hukuncin dakatar da taron, inda daya ya bayyana cewa an hana Lamido saya fom din takarar shugaban jam’iyyar na kasa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

A babban kotun Jihar Oyo, a cikin karar da magoya bayan gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde suka shigar, ta amince da taron, duk da cewa har yanzu ba a yanke hukunci a mahangar shari’a ba. Bangaren Makinde da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammed sun goyi bayan Kabiru Tanimu Turaki (SAN) a matsayin sabon shugaban jam’iyyar tare da goyon bayan kwamitin amintattu karkashin tsohon shugaban majalisar dattawa, Adolphus Wabara.

Kazalika, jam’iyyar LP, wadda ta zo ta uku a zaben shugaban kasa na 2023, ta shiga rikicin shugabanci mai tsawo. Bangarori masu hamayya sun yi amfani da hukuncin kotu daban-daban don tabbatar da sahihancinsu, har ma suna kin bin hukuncin kotun koli wajen warware rigingimun. Masana na gargadi cewa wannan ci gaba da rikici na iya raunana damar jam’iyyar wajen shirya zaben fid da gwani da kuma fitar da ‘yan takara masu inganci a shekarar 2027.

Ita ma sabuwar jam’iyyar NNPP, wadda ta zo ta hudu a 2023, na fuskantar irin wannan rikici. Hukuce-hukuci kotuna da dama sun amince da rassan daban-daban, wanda ya sa ayyukan jam’iyyar sun tsaya cak.

Jam’iyyar ADC, wadda yanzu ke karkashin jagorancin hadin gwiwar ‘yan adawa, tana fama da rikice-rikicen shari’a na cikin gida. Tsohon dan takarar shugaban kasa, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci hadi gwiwar jam’iyyar a gaba kotu, inda har yanzu ba yanke hukunci ba, abin da ke nuna irin mawuyaci hali da jam’iyyar za ta iya fadawa kafin 2027.

A farkon wannan shekara ce, kotun koli ta yanke hukunci da nufin warware rikice-rikice na cikin gida a cikin PDP da LP, amma lamarin ya ci tura. Kotun kolin ta jaddada cewa al’amuran cikin gida na jam’iyya, ciki har da neman takarar shugabanci, galibi suna karkashin kundin tsarin jam’iyya kuma ba sa karkashin hukuncin kotu, sai in har an take hakkokin Dan’adam. Duk da haka, hukunce-hukunce masu karo da juna na kananan kotuna sun raunana wannan ka’ida, inda masana shari’a suka danganta hakan ga juya hukunci a kotuna.

Kotu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
Kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Kotu
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

An Jinjinawa Dabarun Kasar Sin Na Ci Gaban Noma Da Ciniki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.