ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Kawance

A yayin da tattaunawar kawancen ‘yan adawa ke ci gaba da gudana domin kalubalantar Shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, masu ruwa da tsaki a yankin arewa na kara matsa kaimi wajen duba yiwuwar yarjejeniyar zakulo dan takarar shugaban kasa da zai yi wa’adi daya a yankin kudu.

Wata majiya mai ruwa da tsaki a tattaunawar gamayyar jam’iyyun adawa wadda ta bukaci a sakaya sunanta saboda rashin ba da izinin yin magana a kan lamarin, ta shaida wa manema labarai cewa masu ruwa da tsaki a yankin arewa na neman tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ka da ya tsaya takara.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Sin Ta Bayyana Wani Shiri Na Bunkasa Kiwon Lafiya

Majiyar ta kara da cewa mafi yawan masu ruwa da tsaki na ganin cewa idan dukkanin shugabannin kawancen suka hada kai tare da mara wa dan takara a yankin kudu baya, za su iya kayar da Shugaba Tinubu.

ADVERTISEMENT

A ranar 20 ga Maris, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku da Peter Obi na jam’iyyar LP da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun sanar da kafa kawancen da ke da nufin kwace mulki a wurin Shugaba Tinubu a shekarar 2027.

Ana ci gaba da tafka muhawara kan ko ya kamata jam’iyyun adawa su hada kai don kalubalantar gwamnatin Shugaba Tinubu’, inda ‘yan siyasa daban-daban ke musayar ra’ayoyi daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku ya kasance mai fafutukar tabbatar da hadin kan ‘yan adawa, yana mai jaddada muhimmancin hadin gwiwa wajen kayar da Tinubu a zaben 2027.

A ranar 8 ga watan Maris ne ya bayyana kokarinsa na hada kan ‘yan adawa da kafa kawancen korar jam’iyyar APC.

Bayan sauya shekar El-Rufa’i daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PSP a ranar 10 ga watan Maris, tattaunawar da aka yi tsakanin shugabannin ‘yan adawa ta samu gagarumar nasara.

Atiku da sauran ‘yan adawa sun bayyana cewa taron na ranar 20 ga watan Maris ya nuna kaddamar da kawancen a hukumance.

A baya dai an ruwaito a ranar 23 ga watan Maris cewa ana jinkirin tattaunawa kawance tsakanin shugabannin siyasa saboda burin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku na tsayawa takara da kuma rikicin shiyya.

Majiya ta bayyana cewa masu ruwa da tsaki suna da zabi da yawa don magance duk abubuwan da lamarin ya kunsa.

Majiyar ta ce, “Akwai batutuwa da dama a tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki a tattaunawar kawancen, inda batun arewa da kudu shi ne babban abin da ya fi daukar hankali.

“Yawancinmu mun fahimci cewa idan muka tsayar da dan takarar kudu wanda ya cancanta kuma mai gaskiya, kayar da Shugaba Tinubu zai fi sauki. Don haka da yawa daga cikin masu ruwa da tsaki, musamman na arewa, suna kira ga Atiku a kan kar ya tsaya takara, ya bai wa kawancen damar mara wa dan takarar kudancin kasar nan baya da zai yi wa’adi daya idan aka zabe shi.

“A hakika, wasu daga cikin wadannan masu ruwa da tsaki sun dagewa cewa duk wani dan takara daga kudu da za su mara masa baya dole ne ya amince da alkawarin wa’adi daya.

“Wadannan al’amura sun kunno kai, amma mun himmatu wajen magance su a lokacin da suka taso da kuma daukar nauyin ‘yan Nijeriya da dama da suke fuskantar rashin iya shugabancin APC. Manufarmu ita ce tabbatar da ingantaccen tsari wanda ke wakiltar muradun jama’a da karfafa hadin kan kawancen.”

A lokacin da aka yi yunkurin jin ta bakinsa, sakataren kungiyar hadin kan jam’iyyun siyasa ta kasa, Peter Ahmeh, ya tabbatar da cewa masu ruwa da tsaki na yin la’akari da shawarar fitar da dan takara daga kudancin kasar nan tare rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta wa’adi guda.

Ahmeh ya bayyana cewa, kawancen ‘yan adawar da ke adawa da Shugaba Tinubu sun fi wadanda tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan ya fuskanta a shekarar 2014.

Ya ce, “Rattaba hannu kan yarjejeniyar wa’adi guda da dan takara daga kudu na daga cikin abin da ke kan teburin tattauwar, amma har yanzu ba a kammala hakan ba. Bai kai ga karshe ba.

“Peter Obi da wasu masu neman takar shugaban kasa a kudu suka cikin wannan tattaunawa. Na yi imanin cewa za a cimma matsaya nan da ‘yan makonni masu zuwa.

“Akwai zabi masu yawa a kan tebur. Mutane suna kawo sauye-sauye daban-daban, amma gaskiya har yanzu ba a cimma matsaya ba. Da zaran an cimma matsaya kan wannan yarjejeniyar, za mu sanar da al’umma.

“A bayyane yake cewa ‘yan Nijeriya da yawa sun fahimci cewa wannan gwamnati tana cutar da mu fiye da alherinta. Don haka, ‘yan Nijeriya da dama ne ke shiga kawancen. Akwai ‘yan adawa da ke adawa da wannan gwamnati fiye da yadda ake yi wa tsohon shugaban kasar Jonathan a shekarar 2014.

“Don haka, ina kira ga dukkan masu ruwa da tsaki na kkwancen da sauran shugabannin ‘yan adawa da su ci gaba da wannan alkawari domin mu hada kai don ceto kasar nan daga gazawar APC.”

Lokacin da aka tuntubi tsohon mataimakin shugaban kasar, Atiku kai ji ta bakinsa kan wannan kawance, ya yi gargadi game da rade-radin da ka iya kawo cikas ga tattaunawar kawancen.

Atiku, ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya jaddada cewa duk wata yarjejeniya da aka kulla za ta kasance wajibi ga dukkan bangarorin da abin ya shafa.

Shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Shehu Gabam ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntubar juna a fadin kasar nan kan wannan kawancen ‘yan adawa.

Sai dai kuma shugaban matasan jam’iyyar PDP, Timothy Osadolor, ya soki yunkurin da ake yi na dan kudu ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta wa’adi daya, yana mai cewa lamarin ba mai yiwuwa ba ne.

Da yake mayar da martani kan kawancen ‘yan adawa, Daraktan Yada Labarai na APC, Bala Ibrahim, ya yi watsi da yunkurin kawancen, inda ya bayyana cewa farin jinin jam’iyya mai mulki a tsakanin ‘yan Nijeriya na karuwa.

Kawance
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Har Yanzu Shugabanci NNPP Na Hannunmu – Tsagin Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.