A wannan tattaunawar da wakilinmu Muhammad Baƙir Bello ya yi da Ahmad Shu’aibu Isa, shugaban wata ƙungiya mai fafutukar wayar da kan al’umma a kan harkokin siyasa, ya jawo hankain al’umma a kan irin shugaban da ya kamata su zaɓa da kuma yadda za su guji sayar da kuri’un su a zaɓen da ke tafe na 2027. Ga dai yadda hirar ta kasance.
Za mu so ka gabatar mana da kan ka.
Assalamu Alaikum. Sunana Ahmad Shu’aibu Isa, kuma ni ne Shugaban Tafiyar MIDA (Moɓement for Inclusiɓe Deɓelopment Alliance) ƙarƙashin ICRP (Initiatiɓe for Conciliation and Right Protection).
Ganin harkokin siyasa na ƙara kankama a ƙasar nan, wanne irin shugaba kake fatan ya jagoranci Nijeriya?
A ra’ayina, Nijeriya tana buƙatar shugaba mai gaskiya, riƙon amana, adalci, da hangen nesa. Shugaban da zai fifita muradun ƙasa da jin daɗin al’umma fiye da nasa muradun kansa. Ya kasance mai iya magance matsalolin rashin tsaro, rashin aikin yi, talauci, da kuma ƙarfafa fannoni kamar ilimi, lafiya, noma, tattalin arziki da abubuwan more rayuwa. Haka kuma, ya zama shugaba mai haɗa kan al’umma ba tare da nuna bambanci na ƙabila, addini ko yanki ba.
Wanne shawara kake da shi ga al’umma wajen cimma wannan burin?
Shawarata ga al’umma ita ce su yi amfani da ƙuri’arsu cikin hikima. Kada a zaɓi shugaba saboda son zuciya, kuɗi, ƙabila ko addini kawai. A duba cancanta, nagarta, tarihin aiki da irin mafitar da ɗan takara yake bayarwa ga matsalolin ƙasa. Idan muka zaɓi shugabanni bisa cancanta, za mu samu ingantacciyar shugabanci da ci gaba mai ɗorewa.
Mene ne shawarar ka ga ƴan siyasa wajen gudanar da yaƙin neman zaɓe mai tsafta tare da kauce wa kalaman ɓatanci?
Siyasa ba taƙaddama da gaba ba ce, hanya ce ta gabatar da manufofi da neman amincewar jama’a. Ina kira ga ƴan siyasa da su gudanar da yaƙin neman zaɓe cikin mutunci, su guji kalaman ɓatanci, ƙarya, tunzura jama’a da haddasa rikici. Su mayar da hankali wajen bayyana shirye-shiryensu da manufofinsu domin al’umma su tantance su cikin adalci.
Ko kana da saƙo na musamman ga al’umma?
Saƙona ga al’ummar Nijeriya shi ne mu kasance masu haɗin kai, zaman lafiya da kishin ƙasa. Mu kiyaye dokoki, mu mutunta ra’ayoyin juna, kuma mu zaɓi shugabanni bisa gaskiya da cancanta. Idan muka haɗa kai muka fifita muradun ƙasa, za mu gina Nijeriya mai adalci, ci gaba da wadata ga kowa.
Muna godiya
Na gode ƙwarai.














