ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Amurka

Watakila shugaban kasar Amurka Donald Trump yana son wasan kati, saboda yana yawan ambatonsa. Ya taba bayyana wa takwaransa na kasar Ukraine Vladimir Zelenski cewa, ” Ba ka da kati a hannunka, saboda haka ba za ka ci nasara ba. ” Kana a kwanan nan, shugaba Trump ya ce kungiyar kasashen Turai ta EU za ta “nuna sassauci” ga kasar Amurka, dangane da batun cinikayya, saboda Amurka ta rike “dukkan katunan da take bukata”.

Kasancewarsa shugaban wata babbar kasa mai karfi, Mista Trump na kallon kansa a matsayin “mai rike da dimbin katuna masu kyau”, wanda yake iya kalubalantar kasashen duniya. Saboda haka, kasar Amurka ta kaddamar da yakin haraji, inda ta sanar da karbar karin harajin fito kan kayayyakin wasu kasashe 76. Sa’an nan, matakin da Amurka ta dauka, ya sa kasar Sin mayar da martani.

  • Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Bayan Sin da Amurka sun kakaba wa juna wasu matakai na karbar karin harajin fito, kasar Amurka ta fahimci zai yi wuya ta kai labari, don haka ta gayyaci kasar Sin su koma teburin shawarwari, inda kasashen biyu suka daddale yarjejeniyar rage harajin fito. A wajen “wasan kati” na wannan karo, kasar Sin ta ci nasara, in ji kafofin watsa labaru na kasar Amurka. Inda kamfanin dillacin labaru na Bloomberg na kasar Amurka ya ce, “Matakai masu karfi da kasar Sin ta mayar wa kasar Amurka sun yi amfani, inda suka sanya Amurka ja da baya, da bai wa Sin damar samun biyan bukata a harkar cinikayya.”

ADVERTISEMENT

Ko da yake, ba za mu ce “wasan kati” da kasar Amurka ta kaddamar ya riga ya kai karshe ba, amma za mu iya samun wasu fasahohi, bisa nazari kan yadda kasar Sin da sauran kasashe suka yi cudanya da kasar Amurka.

Da farko, idan ana da kati a hannu, sai a dauki mataki ba tare da wata-wata ba.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Tsohon shugaban kasar Sin marigayi Mao Zedong ya taba bayyana cewa, ” Idan an dauki mataki mai karfi wajen neman zaman lafiya, to, za a samu. Amma idan an nuna sassauci a kokarin neman tabbatar da zaman lafiya, to, ba za a samu biyan bukata ba. ” Wannan tunani ya sa kasar Sin nuna ra’ayin kin amincewa da matakin kasar Amurka na karbar karin harajin fito ba tare da wasiwasi ba. Musamman ma ta la’akari da yadda kasar ba ta rasa “kati” a hannunta ba, inda karfin tattalin arzikinta, da manufar bude kofa da ta dauka, dukkansu suka kasance karfinta na tinkarar kalubale.

Sai dai, idan babu “kati” a hannu, yaya za a yi? Ga shi, abu na biyu da ya kamata mu lura da shi, shi ne, yayin da muke fuskantar matsin lamba daga kasar Amurka, kar mu yi kasa a gwiwa, maimakon haka ya kamata mu yi kokarin hadin gwiwa da abokan hulda.

Bayan da kasar Amurka ta kaddamar da yakin haraji, kasar Japan ita ce kasa ta farko da ta tura wakili zuwa kasar Amurka, don rokon a yafe mata harajin da aka kara. Amma ba ta samu komai ba, ta tashi a fankan-fayau balle ma a batun harajin kwastam mai matukar tsanani. Ganin haka ya sa kasar Japan ita ma ta dauki “kati”, ta fara wasa da shi, inda kasar ta sanar da cewa ba za ta taba hakuri da manufar haraji ta kasar Amurka ba. Kana jaridar Labarun Tattalin Arziki Na Kasar Japan ta wallafa wani bayani mai taken “Matakan Kasar Amurka Za Su Haifar Da Tsarin Cinikin Duniya Da Bai Kunshi Kasar Amurka Ba”.

A hakika, ana kan hanyar samun wani tsarin cinikin duniya, da bai shafi kasar Amurka ba, ko kuma ba zai tasirantu da Amurka ba. Idan mun lura da ayyukan da dimbin kasashen nahiyoyin Asiya, da Afirka, da Latin Amurka suke yi, da sanarwoyin kasashen BRICS, da na kungiyar kasashen Afirka ta AU, to, za mu san cewa, kasashe masu tasowa suna kokarin karfafa hadin kansu a fannin tattalin arziki da cinikayya, da daidaita tsare-tsaren samar da kayayyaki, ta yadda za su samu sabbin damammakin raya kansu, yayin da ake fuskantar daidaituwar yanayin tattalin arzikin duniya.

Haka zalika, wata shawara mafi muhimmanci ita ce, a yi watsi da burin zama abokiyar kasar Amurka.

Saboda Amurka na kallon moriyar kanta a gaba da komai. Don haka, idan wata kasa tana son zama abokiyar huldar kasar Amurka, to, wata rana za ta ga yadda kasar Amurka ta mai da ita tamkar abokiyar gaba. Wannan dabarar kasar Amurka ta sa Ukraine rasa albarkatun kasarta, kana kasar Canada ta zama “jiha ta 51 ta kasar Amurka” a idon Amurka din. Yayin da kasashen Turai, ko da yake suke son taimakon kasar Amurka wajen dakile tattalin arzikin Sin, sai dai duk da haka, kasar Amurka na son ganin yadda kasashen Turai su nuna sassauci, da zama wani bangaren da kasar Amurka za ta iya kwatar dukiyoyinsa yadda ta ga dama. (Bello Wang)

Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na'ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.