ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Amurka

Watakila shugaban kasar Amurka Donald Trump yana son wasan kati, saboda yana yawan ambatonsa. Ya taba bayyana wa takwaransa na kasar Ukraine Vladimir Zelenski cewa, ” Ba ka da kati a hannunka, saboda haka ba za ka ci nasara ba. ” Kana a kwanan nan, shugaba Trump ya ce kungiyar kasashen Turai ta EU za ta “nuna sassauci” ga kasar Amurka, dangane da batun cinikayya, saboda Amurka ta rike “dukkan katunan da take bukata”.

Kasancewarsa shugaban wata babbar kasa mai karfi, Mista Trump na kallon kansa a matsayin “mai rike da dimbin katuna masu kyau”, wanda yake iya kalubalantar kasashen duniya. Saboda haka, kasar Amurka ta kaddamar da yakin haraji, inda ta sanar da karbar karin harajin fito kan kayayyakin wasu kasashe 76. Sa’an nan, matakin da Amurka ta dauka, ya sa kasar Sin mayar da martani.

  • Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Bayan Sin da Amurka sun kakaba wa juna wasu matakai na karbar karin harajin fito, kasar Amurka ta fahimci zai yi wuya ta kai labari, don haka ta gayyaci kasar Sin su koma teburin shawarwari, inda kasashen biyu suka daddale yarjejeniyar rage harajin fito. A wajen “wasan kati” na wannan karo, kasar Sin ta ci nasara, in ji kafofin watsa labaru na kasar Amurka. Inda kamfanin dillacin labaru na Bloomberg na kasar Amurka ya ce, “Matakai masu karfi da kasar Sin ta mayar wa kasar Amurka sun yi amfani, inda suka sanya Amurka ja da baya, da bai wa Sin damar samun biyan bukata a harkar cinikayya.”

ADVERTISEMENT

Ko da yake, ba za mu ce “wasan kati” da kasar Amurka ta kaddamar ya riga ya kai karshe ba, amma za mu iya samun wasu fasahohi, bisa nazari kan yadda kasar Sin da sauran kasashe suka yi cudanya da kasar Amurka.

Da farko, idan ana da kati a hannu, sai a dauki mataki ba tare da wata-wata ba.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Tsohon shugaban kasar Sin marigayi Mao Zedong ya taba bayyana cewa, ” Idan an dauki mataki mai karfi wajen neman zaman lafiya, to, za a samu. Amma idan an nuna sassauci a kokarin neman tabbatar da zaman lafiya, to, ba za a samu biyan bukata ba. ” Wannan tunani ya sa kasar Sin nuna ra’ayin kin amincewa da matakin kasar Amurka na karbar karin harajin fito ba tare da wasiwasi ba. Musamman ma ta la’akari da yadda kasar ba ta rasa “kati” a hannunta ba, inda karfin tattalin arzikinta, da manufar bude kofa da ta dauka, dukkansu suka kasance karfinta na tinkarar kalubale.

Sai dai, idan babu “kati” a hannu, yaya za a yi? Ga shi, abu na biyu da ya kamata mu lura da shi, shi ne, yayin da muke fuskantar matsin lamba daga kasar Amurka, kar mu yi kasa a gwiwa, maimakon haka ya kamata mu yi kokarin hadin gwiwa da abokan hulda.

Bayan da kasar Amurka ta kaddamar da yakin haraji, kasar Japan ita ce kasa ta farko da ta tura wakili zuwa kasar Amurka, don rokon a yafe mata harajin da aka kara. Amma ba ta samu komai ba, ta tashi a fankan-fayau balle ma a batun harajin kwastam mai matukar tsanani. Ganin haka ya sa kasar Japan ita ma ta dauki “kati”, ta fara wasa da shi, inda kasar ta sanar da cewa ba za ta taba hakuri da manufar haraji ta kasar Amurka ba. Kana jaridar Labarun Tattalin Arziki Na Kasar Japan ta wallafa wani bayani mai taken “Matakan Kasar Amurka Za Su Haifar Da Tsarin Cinikin Duniya Da Bai Kunshi Kasar Amurka Ba”.

A hakika, ana kan hanyar samun wani tsarin cinikin duniya, da bai shafi kasar Amurka ba, ko kuma ba zai tasirantu da Amurka ba. Idan mun lura da ayyukan da dimbin kasashen nahiyoyin Asiya, da Afirka, da Latin Amurka suke yi, da sanarwoyin kasashen BRICS, da na kungiyar kasashen Afirka ta AU, to, za mu san cewa, kasashe masu tasowa suna kokarin karfafa hadin kansu a fannin tattalin arziki da cinikayya, da daidaita tsare-tsaren samar da kayayyaki, ta yadda za su samu sabbin damammakin raya kansu, yayin da ake fuskantar daidaituwar yanayin tattalin arzikin duniya.

Haka zalika, wata shawara mafi muhimmanci ita ce, a yi watsi da burin zama abokiyar kasar Amurka.

Saboda Amurka na kallon moriyar kanta a gaba da komai. Don haka, idan wata kasa tana son zama abokiyar huldar kasar Amurka, to, wata rana za ta ga yadda kasar Amurka ta mai da ita tamkar abokiyar gaba. Wannan dabarar kasar Amurka ta sa Ukraine rasa albarkatun kasarta, kana kasar Canada ta zama “jiha ta 51 ta kasar Amurka” a idon Amurka din. Yayin da kasashen Turai, ko da yake suke son taimakon kasar Amurka wajen dakile tattalin arzikin Sin, sai dai duk da haka, kasar Amurka na son ganin yadda kasashen Turai su nuna sassauci, da zama wani bangaren da kasar Amurka za ta iya kwatar dukiyoyinsa yadda ta ga dama. (Bello Wang)

Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na'ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.