• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Wasu Manoma A Jihar Kano Suka Ba Da Hayar Gonakinsu

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abin Da Ya Sa Wasu Manoma A Jihar Kano  Suka Ba Da Hayar Gonakinsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da daminar kakar yin noma ta shekarar 2003 ta fara a kasar nan, biyo bayan ci gaba da samun hauhawan farashin takin zamani wasu manoma a jihar Kano sun bayar da hayar gonakansu da wadanda za su iya noma su.

Hauhawan farashin na takin zamani a daukacin fadin kasar nan, na ci gaba da ciwo manoman Tuwo a Kwarya.

  • Tsadar Farashin Irin Hatsi: Har Yanzu Ba Ta Sake Zani Ba – Manoma

Saboda ci gaba hauhawan farashin manoman na ganin ba za su iya mayar da kudaden da suka kashe wajen yin noman ba, ballabta na har su samu wata ribar kirki bayan sun yi noman.

Lamarin na hauhawan farashin har ya fi yin kamari ga kananan manoman, inda wasu daga cikin manoman ma, suka gwammace su daina yin noman ko kuma su rage yin noma a gonakansu a kakar noman ta bana kamar yadda suka saba yi a baya.

Wasu manoma sun ce, farashin takin zamani samfarin NPK 20-10-10 akasari ana sayar da shi daga Naira 15,000 zuwa Naira 17,000.
Sun kara da cewa, ana kuma sayar da takin zamani samfarin Urea daga Naira 21,000 zuwa Naira 22,000.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

A cewarasu, ana kuma sayar da takin zamani samfarin Golden NPK kan Naira 25,000.
Sun bayyana cewa, idan aka yi lissafi karamin manomi da ke da a kadada daya ta Shinkafa za ta ci buhunhunan takin zamani akalla takwas, inda jimmlar kudin zai kai Naira156,000.

Bisa ga kididdigar da Cibiyar bunkasa takin zamani ta kasa da kasa ya fitar IFDC ta nuna cewa, Nijeriya ta shigo da takin zamani da ya kai metric tan 706,922 a shekarar 2021, inda kuma aka shigo da wasu sanadaran hada takin zamanin 429,303 a shekarar 2020.

“Idan aka yi lissafi karamin manomi da ke da a kadada daya ta Shinkafa za ta ci buhunhunan takin zamani akalla takwas, inda jimmlar kudin zai kai Naira156,000.”
Bugu da kari, a farkon mulkin gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, gwamnatin ta kulla yarjejeniya da wasu kamfanonin kasar nan da ke sarrafa takin zamani domin su shigo da kayan da ake hada takin daga kasashen Morocco, Rasha da Ukraine domin a sayar wa manoman a farashi mai sauki.

A yayin da gwamnatin Buhari ta fara yin amfani da wannan tsarin ta hanyar shirin takin zamani ma fadar shugaban kasa (PFI), hakan ya taimaka wajen rage farashin na takin zamani, inda kuma hakan, ya taimaka wa manoman kasar nan matuka.

Dakta Farouk Hamzat, wani mai kamfanin sarrafa takin zamani a jihar Kano ya bayyana cewa, hukuncin da gwamnatin tarayya ta yanke na dakatar da shirin na PTI ne ya janyo ci gaba da hauhawan farashin takin zamanin, indabya yi nuni da cewa, farashin zai ci gaba tashi idan har gwamnatin tarayya ba shiga tsakani ba.

“Hukuncin da gwamnatin tarayya ta yanke na dakatar da shirin na PTI ne ya janyo ci gaba da hauhawan farashin takin zamanin, indabya yi nuni da cewa, farashin zai ci gaba tashi idan har gwamnatin tarayya ba shiga tsakani ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Gwammace Zama Mashawarci A Gefe, Ba Shugaban Ma’aikatan Tinubu Ba – El-Rufai

Next Post

Sudan: Kashi Na Uku Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja 

Related

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

6 days ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

6 days ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

3 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

3 weeks ago
Next Post
Sudan: Kashi Na Uku Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja 

Sudan: Kashi Na Uku Na 'Yan Nijeriya Sun Iso Abuja 

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.