Wani makusanci ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Jafaru Ibrahim Sani, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar ADC gabanin zaɓen 2027.
Jafaru Sani, wanda ya taɓa zama kwamishinan ƙananan hukumomi da harkokin masarautu sannan daga baya kwamishinan ilimi a gwamnatin tsohon gwamna Nasir El-Rufai, ya riga ya karɓi fom ɗin takarar gwamna ta jam’iyyar.
Rahoton Daily Trust ta bayyana cewa, bayan tuntuɓarsa ta WhatsApp, ya tabbatar da matakin nasa cikin gajeren saƙo inda ya ce: “Muna ƙoƙarin kasancewa cikin masu neman takarar. Allah Ya yi mana jagora.”
Rahotanni sun nuna cewa a ranar Laraba an gan shi tare da sauran masu neman takarar gwamna a wani taro inda suka amince da yin aiki tare domin ganin jam’iyyar ADC ta samu nasara a zaɓen 2027.
Sauran waɗanda ke neman takarar gwamna a jam’iyyar sun haɗa da Isah Ashiru Kudan, Farfesa Muhammad Sani Bello, Shuaibu Idris Mikati da kuma Tijjani Ahmad.















Discussion about this post