ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
APC

Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda shi ne sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, bayan amincewar taron NEC na 14 da aka gudanar a ranar Alhamis. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar ke ƙoƙarin sake daidaita kanta domin tunkarar ƙalubalen ciki da na zaɓen 2027.

An haifi Yilwatda a ranar 8 ga watan Agusta, 1968 a Dungung, ƙaramar hukumar Kanke ta jihar Filato. Ya yi karatu a Boys’ Secondary School Gindiri, sannan ya samu digiri na farko daga Jami’ar Noma ta Tarayya da ke Makurdi, sai digiri na biyu daga Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi, da kuma digirin digirgir daga Jami’ar Nijeriya Nsukka a fannin Injiniyan Kwamfuta da Na’ura.

  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  • Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

Yilwatda ya yi aiki na fiye da shekaru 26 a Jami’ar Makurdi inda ya kai matsayin Darakta na farko a sashin ICT na jami’ar, inda ya jagoranci sauye-sauyen fasaha masu zamani. Ya kuma yi aiki da hukumomin ƙasa da ƙasa kamar EU, da UNICEF, da World Bank da TECHVILE USA, yana ba da shawarwari a fannin cigaban fasaha da shugabanci.

ADVERTISEMENT

A 2017, an naɗa shi a matsayin kwamishinan zaɓe a hukumar INEC, inda ya jagoranci sauye-sauyen tsarin kaɗa ƙuri’a musamman ga ‘yan gudun hijira da masu buƙata ta musamman. Daga bisani ya sauka daga kujerar domin shiga siyasa, inda ya tsaya takarar gwamnan Filato ƙarƙashin APC a 2023, kuma ya jagoranci kamfen na Tinubu/Shettima a jihar.

Tun kafin naɗinsa a matsayin shugaban jam’iyya, Yilwatda yana rike da muƙamin Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, da kuma mamba a kwamitin tattalin arziƙin shugaban ƙasa. Kwarewarsa a fannin fasaha da shugabanci na ƙara tabbatar da cewa yana da cancanta a matsayin sabon jagoran jam’iyyar APC.

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

APC
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Mutane 31 A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kano Ta Kulle Shagon Maganin Gargajiya Saboda Batsa
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Gurfanar Da Jami’in NDLEA Bisa Zargin Yi Wa Yarinya Fyaɗe

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026
Manyan Labarai

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
APC

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
APC

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.