Lamarin tsaro ya sake taɓarɓarewa a Jihar Katsina biyo bayan wani sabon hari da ’yan bindiga suka kai kan wani ƙauye, inda suka kashe mutum ɗaya tare da sace mutane 31.
Wani rahoto ya tabbatar, maharan sun farmaki al’ummar ne a cikin tsakar dare suna harbe-harbe ta kowane ɓangare domin tsoratar da mazauna yankin da hana su samun damar guduwa ko a kawo musu ɗauki.
Sakamakon harbin da maharan suka riƙa yi ta ko ina, mutum ɗaya ya rasa ransa a take, yayin da ’yan fashin dajin suka tara mata da ƙananan yara har da maza guda 31 suka yi awon gaba da su zuwa cikin daji.
Mazauna yankin sun yi kiran gaggawa zuwa ga rundunar ’yansanda da sauran jami’an tsaro na Jihar Katsina domin gudanar da bincike mai zurfi tare da aikawa da dakarun tsaro cikin daji don ceto mutanen da aka sace.
Wannan hari dai na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummomi da dama a yankunan karkara na Jihar Katsina ke ci gaba da fuskantar matsin lamba da barazana daga ɓangaren ’yan bindiga, wanda ke buƙatar gaggauta tsaurara matakan tsaro.














